• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Thursday, July 24, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Gwamnati ta fara biyan bashi ga mutum 14,021 ‘yan kashi na ‘A’ da ‘B’ na shirin N-Power

by DAGA WAKILIN MU
September 18, 2021
in Nijeriya
0
Hajiya Sadiya Umar Farouq

Hajiya Sadiya Umar Farouq

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MA’AIKATAR Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa ta Tarayya ta bayyana cewa a yanzu ta fara yin biyan ƙarshe na bashin da ya rage ga masu cin moriyar shirin tallafi na N-Power kashi na ‘A’ da ‘B’ su 14,021.

Hakan ya biyo bayan kammala warware ‘yar mishkilar da aka samu a tsarin da ake amfani da shi wajen tattara bayanan biyan kuɗin.

Babban Sakataren ma’aikatar, Alhaji Bashir Nura Alƙali, shi ne ya bayyana haka a cikin wata takarda ga manema labarai da ya saki a Abuja a madadin ministar ma’aikatar, wato Hajiya Sadiya Umar Farouq.

Alƙali ya ce tun a cikin watan Maris 2020 ne asusun ajiya na masu cin moriyar shirin su 14,021 su ka samu matsala, inda tsarin biyan kuɗin na Gwamnatin Tarayya mai suna ‘Integrated Financial Management Information System’ (GIFMIS) ya dakatar da biyan nasu kuɗin saboda wasu dalilai daban-daban waɗanda su ka haɗa da:

1) mallakar asusun banki sama da ɗaya na masu cin moriyar shirin, da kuma

2) karɓar wasu kuɗin daban a asusun banki na masu cin moriyar shirin kamar su albashi da alawus-alawus daga ma’aikatu da cibiyoyin Gwamnatin Tarayya daban-daban, na aikin dindindin ko na wasu shirye-shiryen da su ka shiga.

Ya ce waɗannan hidindimun sun saɓa wa ƙa’idojin shirin sa-kai na N-Power wanda ka iya jawo babban laifi da ma cin hanci da rashawa.

Babban Sakataren ya ƙara da cewa ma’aikatar ta yi wani bincike mai zurfi tare da haɗin gwiwar ma’aikatun gwamnati da su ka dace kuma zuwa yanzu an warware mishkilar da ta shafi asusun mutum 9,066 ‘yan sa-kai a shirin, kuma har an fara biyan su. 

Ya ce, “Bisa ga wannan tantancewar, yanzu an soma biyan alawus ɗin watanni biyar da waɗannan ‘yan sa kan ke bi, kowanne wata a kan jimillar N150,000.00. Alawus ɗin sauran mutum 4,955 kuwa an riƙe su har zuwa lokacin da za a kammala binciken da ake yi. 

“Idan an tabbatar mutum ya karya ƙa’idojin yarjejeniyar da aka yi, to za a yi wa irin waɗannan masu karya ƙa’idar hukuncin da ya kamata kamar yadda doka ta tanada.”

Haka kuma Alƙali ya ce akasin surutun da ake yaɗawa a cikin jama’a, wannan tsari babbar manuniya ce ta irim ƙoƙarin da ma’aikatar ke yi na ganin ta magance wannan matsala maras daɗi da aka samu ta hanya fisabilillahi domin tsare gaskiya tare da kauce wa sake aukuwar hakan a nan gaba. 

Ya ce, “Kamar dai yadda ake ta faɗa, binciken da ma’aikatar ta yi shi ne ya fi dacewa da ƙasar nan kuma babbar manufar sa ita ce a kafa ingantaccen Shirin Inganta Rayuwa na Ƙasa, wato ‘National Social Investment Programme’ (NSIP) tare da tabbatar da cewa ana gudanar da shi cikin aminci kamar yadda mai girma Shugaban Ƙasa ya ƙudiri aniyar tabbatar da tsare gaskiya da amana a wajen aiwatar da shirin a kowane lokaci.”

Alƙali ya ce ma’aikatar ba ta ji daɗin tsaikon da aka samu ba wajen kammala wannan tsarin, “to amma ta na tabbatar wa da jama’a cewa ba za ta iya yin watsi da tsare gaskiya da amana ba a dukkan ayyukan ta.”

Loading

Tags: Bashir Nura AlkaliDisaster Management and Social InvestmentMinistry of Humanitarian AffairsN-PowerNational Social Investment ProgrammeSadiya Umar Farouq
Previous Post

Rarara ya yi wa yaran sa biyu kyautar mota da gida

Next Post

Bayan shahara a Kannywood, ina so in zama babbar ‘yar kasuwa – Sadiya Sareena

Related Posts

Sanatan Kaduna: Yerima Shettima za mu yi, inji ‘yan fim
Nijeriya

Sanatan Kaduna: Yerima Shettima za mu yi, inji ‘yan fim

July 15, 2025
Nijeriya

Tinubu yana goyon bayan Ƙananan Hukumomi su ci gashin kan su – Minista

July 11, 2025
Nijeriya

Shirin Sabunta Fata na Tinubu yana samar da damarmakin cigaba — Minista

July 10, 2025
Sauye-sauyen Tinubu suna taimaka wa farfaɗowar tattalin arzikin Nijeriya — Minista
Nijeriya

Sauye-sauyen Tinubu suna taimaka wa farfaɗowar tattalin arzikin Nijeriya — Minista

July 10, 2025
Ministoci za su fara gabatar da rahoton ayyuka a taron manema labarai
Nijeriya

Tinubu ba zai yarda hayaniyar siyasar 2027 ta ɗauke masa hankali ba – Minista

July 8, 2025
Ƙungiyoyi sun buƙaci bayanai daga ‘yan sanda kan harin da aka kai fadar Sarkin Kano
Nijeriya

Ƙungiyoyi sun buƙaci bayanai daga ‘yan sanda kan harin da aka kai fadar Sarkin Kano

July 8, 2025
Next Post
Sadiya Abdulƙadir (Sareena)

Bayan shahara a Kannywood, ina so in zama babbar 'yar kasuwa - Sadiya Sareena

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!