* An karrama Nura M. Inuwa da Falalu Ɗorayi
GWAMNATIN Jihar Kano ta jaddada ƙudirin ta na cigaba da zaƙulo managartan hanyoyi da za su kare martabar harshen Hausa.
Mataimakin Gwamnan jihar, Dakta Nasiru Yusuf Gawuna, shi ne ya bayyana haka a wajen taron kammala gasar kacici-kacici tsakanin manyan makarantun gaba da sakandare da ke faɗin Jihar Kano kan harshen Hausa, wanda Ƙungiyar Ɗaliban Hausa ta Nijeriya tare da haɗin gwiwar Ƙungiyar Muryar Hausawan Duniya ta shirya.
Mataimakin gwamnan ne ya ɗauki nauyin shirya gasar, kuma an gudanar da taron a Jami’ar Bayero, Kano.
A jawabin nasa, Gwuna ya bayyana harshen Hausa da cewa ya yi fice a cikin harsunan duniya.
Ya nanata burin sa na ci gaba da bada gudunmawar sa wajen kare martabar harshen da bunƙasa shi ta hanyar shirya irin wannan gasar.
Gawuna ya ce gwamnatin jihar, a ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, ta maida hankali wajen samar da ilimi tun daga tushe.
Ya ƙara da cewa gwamnatin ta samar da shirin ta na ilimi kyauta kuma dole domin samun al’umma mai nagarta.
Daga nan mataimakin gwamnan ya taya waɗanda su ka samu nasara murna tare da kira ga ɗalibai da su maida hankali ga karatun su domin samun cigaba.

A nasa jawabin, Mataimakin Shugaban jami’ar (VC), Farfesa Sagir Adamu, wanda Farfesa Hafizu Miko ya wakilta, ya yaba da ƙoƙarin Dakta Gawuna bisa kulawar sa ga cigaban ilimi a jihar.
Wakilin mujallar Fim ya shaida mana cewa a yayin gasar dai Kwalejin Ilimi ta Tarayya (FCE) ce ta zo ta ɗaya, sai Jami’ar Bayero da ke biye mata a matsayin ta biyu, inda Kwalejin Nazarin Harkokin Shari’a ta Kano ta zo ta uku.
A taron, an karrama babban mawaƙi Nura M. Inuwa da fitaccen darakta kuma mashiryin diramar ‘Gidan Badamasi’ ta tashar Arewa24, Falalu A. Ɗorayi, da lambar girmamawa sakamakon irin gudunmawar da su ke bayarwa ga cigaban harshen Hausa.
A ƙarshe, mawaƙan Kannywood sun nishaɗantar da jama’ar da su ka halarci taron, ciki har da Nura M. Inuwa da Nura Ɗandolo da kuma wasu mawaƙan hip-hop da ake kira Fresh Emir.
Taron ya samu halartar jaruman Kannywwod irin su Tijjani Asase, Umar M.S. Jigirya, Murtala Karabiti, Ado Ahmad Gidan Dabino, Ɗandolo da sauran su.