• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, August 25, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Gwamnatin Tarayya ta fara sabunta kayan aikin gidajen watsa labarai, cewar Minista

by ABUBAKAR IBRAHIM
April 8, 2025
in Nijeriya
0
Gwamnatin Tarayya ta fara sabunta kayan aikin gidajen watsa labarai, cewar Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris (na 4 daga hagu), tare da shugabannin hukumomin yaɗa labarai na Gwamnatin Tarayya a birnin Las Vegas

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MINISTAN Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta fara zuba jari wajen samar da sababbin fasahohi da na’urorin zamani domin ƙarfafa ayyukan kafafen yaɗa labarai na gwamnati.

Ya bayyana hakan ne a birnin Las Vegas da ke Jihar Nevada ta ƙasar Amurka yayin wata tattaunawa da manyan kamfanonin watsa shirye-shirye a taron Ƙungiyar Ƙasa ta Masu Watsa Shirye-shirye (NAB) 2025 da aka gudanar.

Ya ce wannan zuba jarin zai taimaka wajen sabunta da kuma maye gurbin tsofaffin kayan aiki a tashoshin rediyo da talabijin na Gwamnatin Tarayya.

Domin cimma wannan buri, ministan ya bayyana cewa ma’aikatar sa tana haɗin gwiwa da masana’antun kayan watsa shirye-shirye domin bai wa ‘yan jarida a cikin gida damar cin gajiyar sababbin fasahohi da horo na musamman da ya shafi sana’ar su.

Ministan ya jaddada ƙudirin Gwamnati na yin aiki tare da muhimman abokan hulɗa a fannin watsa labarai da sadarwa a duniya domin ƙarfafa tsarin yaɗa labarai a Nijeriya.

Ya ce: “Sadarwa na da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da cewa manufofin Ajandar Sabunta Fata sun isa ga al’ummar Nijeriya yadda ya kamata.”

A yayin taron, Minista ya kai ziyara wuraren da ake baje-kolin kayayyakin zamani da suka haɗa da eriyoyi, na’urorin aika sigina (tiransimita), da kayan aikin situdiyo – duk waɗanda ke da matuƙar muhimmanci wajen inganta watsa shirye-shirye.

Waɗansu daga cikin shugabannin kamfanonin da suka gana da ministan sun haɗa da Shugaban KINTRONIC Laboratories, Thomas King; da Shugaban Axel Technology SRL, Enrico Vaccari; da Shugaban SYES SRL, Gianluca Baccalini; da Shugaban Kintronic Labs Inc, Josh King; Shugaban Thomson Broadcast, Khiran Keerodhur, da Shugaban Continental Electronics, Calvin Carter.

Dukkan su sun nuna a shirye suke su haɗa gwiwa da Gwamnatin Tarayya domin haɓaka harkar watsa labarai da kuma ƙarfafa hukumomin da ke da alhakin tsarawa da sa ido.

A tawagar da Idris ya jagoranta zuwa Amurka ɗin akwai manyan jami’an hukumomin yaɗa labarai na Nijeriya da suka haɗa da Darakta-Janar na NTA, Salihu Abdulhamid Dembos; Manajan-Daraktan Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN), Ali Muhammad Ali; Darakta-Janar na Hukumar Kula da Tashoshin Rediyo da Talbijin (NBC), Charles Ebuebu; Shugaban Hukumar Kula da Harkar Tallace-Tallace ta Ƙasa, (ARCON), Dakta Lekan Fadolapo; da Darakta-Janar na tashar Muryar Nijeriya (VON), Jibrin Baba Ndace.

Idris a tsakiyar wasu jami’an da ya yi tafiyar da su

Taron na NAB, wanda aka gudanar daga ranakun 5 zuwa 9 ga Afrilu, 2025, yana da taken, “Fasaha, Salo da Makoma”, inda aka tattauna batutuwan zamani kamar Ƙirƙirarriyar Basira (AI), bayyanar bayanai ta hanyar fasahar girgije, tattalin arzikin masu ƙirƙira, da kuma samar da shirye-shiryen wasanni da watsa su ta intanet.

Loading

Tags: baje-kolihukumomiLas VegasMohammed IdrisTaro
Previous Post

MOPPAN da KAFIGAN sun yi gaisuwar rasuwar Galadiman Kano

Next Post

Ministan Labarai ya ƙaryata rahoton wai ya ce a yi watsi da damuwar Gwamna Zulum kan tsaro

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Ministan Labarai ya ƙaryata rahoton wai ya ce a yi watsi da damuwar Gwamna Zulum kan tsaro

Ministan Labarai ya ƙaryata rahoton wai ya ce a yi watsi da damuwar Gwamna Zulum kan tsaro

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!