ƘUNGIYOYIN Kannywood biyu, wato Motion Picture Practitioners Association of Nigeria (MOPPAN) da Kannywood Film Industry Guilds and Associations (KAFIGAN), sun miƙa saƙon alhinin su ga iyalan Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sanusi, kan rasuwar sa.
Shi dai Galadima, Allah ya yi masa rasuwa ne jiya yana da shekara 92 bayan ya yi fama da rashin lafiya.
Dattijon , wanda ya fi kowa tsufa a cikin masu riƙe da muƙamin sarauta a masarautar Kano, ya bar ‘ya’ya da jikoki masu yawa. Ɗaya daga cikin ‘ya’yan sa shi ne Shugaban jam’iyyar APC ta Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas.
A cikin takardar sanarwar da MOPPAN ta fitar ta hannun jami’in ta na yaɗa labarai, Malam Ibrahim Amarawa, ƙungiyar ta ce: “Al’ummar Kannywood sun samu labari maras daɗi na rasuwar marigayi Galadiman Kano Alh Abbas Sanusi. Rasuwar sa ba kurum babban rashi ne ga Masarautar Kano ko Jihar Kano kaɗai ba har ma ga Nijeriya baki ɗaya.
“Muna addu’ar Allah maɗaukakin sarki ya gafarta masa kuma ya ba iyalin sa da masoyan sa da dukkan jama’ar Jihar Kano haƙurin jure wannan babban rashin.”
A nata ɓangaren, ƙungiyar KAFIGAN ta fitar da sanarwa ta hannun Daraktan ta na Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a, Malam Al-Amin Ciroma, a Abuja, inda ta ce: “Cikin zurfin baƙin ciki, ƙungiyar Kannywood Film Industry Guilds and Associations (KAFIGAN) tana miƙa saƙon gaisuwar ta kan rasuwar Alhaji Abbas Muhammadu Sanusi, wato Galadiman Kano kuma babban mai zaɓen sarki a Masarautar Kano.”
A takardar, an ruwaito ciyaman na kwamitin amintattu na ƙungiyar, Alhaji Isma’il Na’Abba (Afakallahu), yana bayyana mariganyin da cewa “babban ginshiƙi ne ga tsarin sarautar gargajiya, wanda gudunmawar da ya bayar ga ɗorewar ta da cigaban ta za a ci gaba da tuna su har ma a wajen Masarautar Kano.”
Afakallahu ya miƙa gaisuwar sa ga gwamnati da jama’ar Jihar Kano, da majalisar Sarki da dukkan iyalin mamacin, muna addu’ar Allah ya jiƙan sa ya saka masa da gidan Jannatul Firdaus.
A wani labarin kuma, KAFIGAN ta miƙa saƙon ta’aziyya ga Babban Darakta na Hukumar Tace Finafinai da Ɗabi’i ta Jihar Kano, Alhaji Abba El-Mustapha, bisa rasuwar kakan sa, Malam Kawu Na Warure, wanda ya rasu a yau sakamakon rashin lafiya.
A wata takardar sanarwar da Ciroma ya bayar, an ambato Darakta-Janar na ƙungiyar, Hon. Adamu Bello, a madadin kwamitin amintattu da membobin ƙungiyar, ya miƙa saƙon ta’aziyya ga El-Mustapha kuma ya yi addu’ar Allah ya jiƙan kakan nasa.

![]()






