• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Thursday, July 24, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

INEC na buƙatar N305b domin shirya zaɓen 2023

by DAGA WAKILIN MU
December 22, 2021
in Nijeriya
0
Farfesa Mahmood Yakubu

Farfesa Mahmood Yakubu

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HUKUMAR Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta buƙaci ta gabatar da kasafin naira biliyan 305 ga Majalisar Tarayya domin yin zaɓen 2023 da kuɗaɗen.

Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ne ya gabatar da kasafin ga Kwamitin Kasafin Kuɗi na Majalisar Dattawa, a ranar Litinin.

Kwamitin ya gayyaci INEC da cewa ta sanya kasafin kuɗaɗen da za ta kashe wajen zaɓen 2023 a cikin kasafin kuɗaɗen ta na 2022 domin Majalisar Dattawa da ta Wakilai su yi nazarin kuɗaɗen kuma su amince.

A ranar Talata ne ake sa ran majalisun biyu za su rattaba amincewar su da adadin kuɗaɗen da za a kashe a lokacin zaɓen.

Haka nan kuma Farfesa Yakubu ya yi wa Kwamitin Kasafin Kuɗi bayani dalla-dalla cewa naira biliyan 305 ɗin daban su ke da naira biliyan 40 na kuɗaɗen kasafin shekara na ayyukan yau da kullum a hukumar.

Farfesa Yakubu ya bayyana cewa waɗannan naira biliyan 305 da hukumar ke nema, daban su ke da naira biliyan ɗin da INEC ɗin za ta kashe wajen ayyukan ofishin ta na cikin kasafin 2022.

Yakubu ya ce an rigaya an damƙa wa INEC naira biliyan 100 domin fara shirye-shirye, waɗanda ya ce adadin sun yi kaɗan a fara shirye-shiryen zaɓen 2023 da su.

“Mun damƙa masu kasafin naira biliyan 305 domin aikin zaɓen 2023 da su,” inji shi.

Bayanan kasafin dai ya ƙunshi shafuka 22. 

Waɗancan naira biliyan 40 kuwa, kuɗaɗen ayyukan yau-da-kullum ne na ofishin INEC, ciki har da gudanar da zaɓukan da a kan gudanar ba lokacin ɗaya da babban zaɓe na ƙasa ba.

Ya ce, “Ya kamata wannan kwamiti ya sani cewa nan gaba akwai zaɓukan cike-gurabu har guda takwas, guda uku zaɓen ɗan Majalisar Tarayya ne, sauran biyar kuma na majalisar dokoki ta jihohi ne.”

Shugaban Kwamitin Kasafin Kuɗaɗe, Sanata Barau Jibrin, ya ce za a saka kuɗaɗen gudanar da zaɓen 2023 a cikin kasafin 2022.

Loading

Tags: 2023 electionsHukumar Zaɓe ta ƘasaINECkasafiMajalisar TarayyaProf. Mahmood Yakubu
Previous Post

Hotuna: Fati Ladan da Yerima Shettima sun cika shekara 8 da aure

Next Post

Yawan masu rajistar zaɓe a Nijeriya sun haura na sauran ƙasashen Afrika ta Yamma – INEC

Related Posts

Sanatan Kaduna: Yerima Shettima za mu yi, inji ‘yan fim
Nijeriya

Sanatan Kaduna: Yerima Shettima za mu yi, inji ‘yan fim

July 15, 2025
Nijeriya

Tinubu yana goyon bayan Ƙananan Hukumomi su ci gashin kan su – Minista

July 11, 2025
Nijeriya

Shirin Sabunta Fata na Tinubu yana samar da damarmakin cigaba — Minista

July 10, 2025
Sauye-sauyen Tinubu suna taimaka wa farfaɗowar tattalin arzikin Nijeriya — Minista
Nijeriya

Sauye-sauyen Tinubu suna taimaka wa farfaɗowar tattalin arzikin Nijeriya — Minista

July 10, 2025
Ministoci za su fara gabatar da rahoton ayyuka a taron manema labarai
Nijeriya

Tinubu ba zai yarda hayaniyar siyasar 2027 ta ɗauke masa hankali ba – Minista

July 8, 2025
Ƙungiyoyi sun buƙaci bayanai daga ‘yan sanda kan harin da aka kai fadar Sarkin Kano
Nijeriya

Ƙungiyoyi sun buƙaci bayanai daga ‘yan sanda kan harin da aka kai fadar Sarkin Kano

July 8, 2025
Next Post
Yawan masu rajistar zaɓe a Nijeriya sun haura na sauran ƙasashen Afrika ta Yamma – INEC

Yawan masu rajistar zaɓe a Nijeriya sun haura na sauran ƙasashen Afrika ta Yamma - INEC

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!