WATA jami’a mai zaman kan ta a ƙasar Togo ta bai wa furodusa a masana’antar finafinai ta Kannywood Abdulrahman Mohammed (Abdul Amart Maikwashewa) digirin girmamawa na dakta.
Jami’ar, mai suna IHIRIS University, ta ba shi digirin ne a wani taro da ta gudanar a muhallin ta a jiya Asabar, 12 ga Nuwamba, 2022.
Sanarwar karramawar, wadda mujallar Fim ta gani, ta ce jami’ar ta karrama Abdul ne sakamakon bibiyar ayyukan sa da ta yi na tsawon shekara 10 inda ta gano cewa shi mutum ne mai son cigaban jama’a, wanda hakan ya sa jama’a da dama su ke ƙaruwa ta hanyar gudunmawar da ya ke ba su, don haka a matsayin sa na mai ciyar da al’umma gaba ta hanyoyin sama musu abin yi da kuma yadda za su dogara da kan su.
Ta ce sgi ne dalilin ba shi digirin domin ya ƙara himma wajen abin da ya sa a gaba.
Tuni dai Abdul Amart ya dawo gida da yammacin wannan rana ta Lahadi.
Abdul Amart, wanda shi ne shugaban ƙungiyar ‘YBN Network Group’, ya yi addu’ar Allah ya sa wannan digiri da aka ba shi ya amfane shi da kuma duniya baki ɗaya.
Ya yi wannan addu’ar ne a yau Lahadi lokacin da ya ɗora hotunan ba shi digirin a Instagram, ya kuma yi rubutu da Turanci ya ce, “On the 12th of Nov, 2022, I was honored by the IHERIS University Togo, with a doctor of philosophy in Diplomacy and Public Management. It is indeed a great honor and as such I will like to thank the management of IHERIS university for this great honor. May Allah almighty make it useful for me and the entire Universe.”
Mujallar Fim ta fassara rubutun da cewa: “Ran 12 ga Nuwamba, 2022, an karrama ni a IHIRIS University, Togo, da digirin girmamawa a ‘Philosophy In Diplomacy and Public Management’. Lallai wannan babbar girmamawa ce, saboda haka zan so in gode wa hukumar gudanarwa ta IHERIS University a kan wannan babbar karramawa. Allah ya sa ta amfane ni da duniya baki ɗaya.”
A yanzu Abdul Amart ya bi sahun su Ali Nuhu, Aminu Ladan Abubakar (ALA) wajen samun digirin girmamawa na dakta.
Ɗimbin ‘yan fim da sauran jama’a sun taya Abdul Amart murna kan wannan abin farin ciki da ya samu.
Ƙungiyar ‘Kannywood Foundation’, wato Gidauniyar Kannywood, ta taya shi murna.

Kakakin ƙungiyar, Alhaji Mohammed Kabiru Maikaba, ya ba da sanarwa cewa: “A madadin shugabancin majalisar ƙoli ta dattawan masana’antar shirya finafinan Hausa ta Kannywood, wato ‘Kannywood Foundation’, na matuƙar farin cikin taya ɗan’uwan mu, Dr. Abdul Muhammed Amart (Maikwashewa) murnar samun wannan ɗaukaka ta samun babbar lambar yabo ta digirin digirgir, wato Doctorate Degree’.
“Hakika dukkan mu a wannan majalisa mun cika da farin cikin samun wannan labari. Sabili da haka, kafatanin shugabanci da ‘ya’yan wannan majalisa na farin cikin taya ka murnar samun wannan zinariyar lamba.
“Babu shakka wannan jami’a ta cancanci yabo don kuwa ta yi wannan abin alheri a gurin da ya dace, don kuwa ta ajiye ƙwarya a gurbin ta. Kuma duk ɗan wannan masana’anta mai albarka ya sani kuma ya ji irin taimako da tallafi da kuma irin gudunmawar da ka ke ba wa ‘ya’yan wannan masana’anta, ‘yan’uwa da dangi da al’ummar Jihar Kano baki ɗaya.
“Babu shakka mutum mai irin zuciyar ka, mutum mai manufar kawo wa al’umma cigaba, ba zai taɓe ba, don haka ba zai ci tuwon sa gaya ba.
“Irin wa’annan manufofi Allah Ubangiji ya duba ya ce wa mala’iku su yabe ka, shi ya sa ka fara ganin sakamakon tun a duniya.
“Dakta! Baki ɗayan mu ‘yan wannan majalisa mu nai maka addu’a Allah ya ci gaba da riƙo da hannun ka. Allah yai maka albarka, ya yi wa zuri’a albarka, ya jiƙan magabata. Allah ya sa wannan cigaba da ka ke samu ya sa danshin sa ya kai ga duk ɗan wannan masana’anta. Allah ya sa wannan yauƙi ya yauƙaƙa ya zuwa duk wani loko da saƙo na wannan masana’anta. Amin. Kafatanin ‘yan wannan majalisa nai maka fatan alheri. Alhamdu lillah.”