• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, August 25, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Jam’iyyu 18 ke fafutikar neman kujerar gwamnan Anambra – INEC

by DAGA WAKILIN MU
June 18, 2021
in Nijeriya
0
INEC ta sa ranakun zaɓen gwamnonin Ekiti da Osun
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HUKUMAR Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ce jam’iyyun siyasa 18 ne su ka nuna sha’awar su ta shiga zaɓen gwamnan Jihar Anambara da za a yi a ranar 6 ga Nuwamba mai zuwa.

Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ne ya bayyana haka a wajen taron kwata ta biyu na hukumar da jam’iyyun siyasa wanda aka yi a ranar Alhamis a Abuja.

Yakubu ya ce dukkan jam’iyyun 18 sun tsara gudanar da zaɓuɓɓukan su na fidda gwani a bisa jadawalin kwanaki da hukumar ta fitar.

Ya ce, “A kan batun zaɓuɓɓukan ƙananan hukumomin Yankin Birnin Tarayya, jam’iyyun siyasa sun gama zaɓuɓɓukan su na share fage a mazaɓu 68 da su ka haɗu su ka yi shugabannin ƙananan hukumomin guda shida da kansiloli 62.

“Jimillar jam’iyyu 14 daga cikin 18 sun zaɓi ‘yan takara 110 na muƙaman Shugaba da Mataimakin Shugaba da kuma ‘yan takarar zama kansila su 362.

“Gaba ɗaya dai, jam’iyyu 14 sun fitar da ‘yan takara 472 da za su nemi kujeru 68 a Yankin Babban Birnin Tarayya.

“Akwai zanen taswira da aka yi mai nuna rabe-raben ƙananan hukumomin a cikin wannan jakar kwalin ta wannan taron da mu ka ba ku.”

Yakubu ya yi kira ga shugabannin jam’iyyun da su riƙa yin kira ga ‘yan takarar su a zaɓen gwamnan da na ƙananan hukumomin da ke Yankin Birnin Tarayya da sauran zaɓuɓɓukan cike gurbin da ke tafe da su tabbatar da zaman lafiya.

Ya ce, “Kamar yadda ku ka sani, akwai zaɓuɓɓukan cike gurbi da na ƙarshen wa’adi da aka shirya gudanarwa kafin Babban Zaɓen 2023.

“A ƙarshen wannan makon, za a yi zaɓuɓɓukan cike gurbi guda biyu a Jihar Kaduna, wato na Mazaɓar Jiha ta Sabon Gari inda jam’iyyu biyar su ka bayar da ‘yan takara, da Jihar Jigawa na Mazaɓar Tarayya ta Gwaram wanda jam’iyyu goma su ka shiga.

“Mun kammala dukkan shirye-shirye na waɗannan zaɓuɓɓukan cike gurbin, wanda ya haɗa da tabbatar da isar muhimman kayan aiki a yau zuwa mazaɓun biyu. Zuwa yanzu dai, babu wata hatsaniya a cikin shirye-shiryen.

“Mu na kira a gare ku da ku ja hankalin ‘yan takara da magoya bayan ku da su ci gaba da tabbatar da zaman lumanar da ke akwai yanzu.

“A game da sauran zaɓuɓɓukan share fage da su ka rage, ina tabbatar maku da cewar da zaran an samu guraben da Kakakin Majalisar Wakilai ya bayyana, za mu fitar da jadawalin lokacin yin su, wato jadawalin lokacin zaɓen Mazaɓar Tarayya ta Jos ta Arewa/Bassa da ke Jihar Filato da na Mazaɓar Tarayya ta Lere da ke Jihar Kaduna.”

Loading

Tags: By-electionsIndependent Electoral CommissionINECProf. Mahmood Yakubu
Previous Post

Kai ma ji kawai ka ke ko ka na fahimta?

Next Post

‘Yan fim sun yi taro kan hana nuno shan sigari a finafinan Nijeriya

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
‘Yan fim sun yi taro kan hana nuno shan sigari a finafinan Nijeriya

'Yan fim sun yi taro kan hana nuno shan sigari a finafinan Nijeriya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!