• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Saturday, June 7, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

KILAF 2020: An yi taron duniya kan finafinan Afrika ba tare da ‘yan Kannywood ba

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
November 25, 2020
in Labarai
0
Alhaji Abdulkareem Muhammad na gabatar da jawabin sa ga taron

Alhaji Abdulkareem Muhammad na gabatar da jawabin sa ga taron

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
AN kwashe tsawon kwana biyu ana gudanar da taron duniya kan finafinan harsunan Afrika na gado, amma masu shirya finanan Hausa ba su halarta ba.

 

A yau ne aka kammala taron a Kano.

A taron, Shugaban Tsangayar Aikin Jarida ta Jami’ar Bayero, Kano, Farfesa Mustapha Nasiru Malam, ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba za a samar da ƙananan kwasa-kwasai a jami’ar domin ƙara wa masu sana’ar shirya fim ilimi.

 
Malamin ya bayyana haka ne a jawabin da ya gabatar bayan  kammala taron yini biyu kan yadda ake gudanar da bincike da rubuta labaran finafinai cikin harsunan Afrika, wanda aka yi a yau a Kano.
 
Taron, wanda aka fi sani da ‘Kano Indigenous Languages of Africa Film Market and Festival’ (KILAF), an gudanar da shi ne ta hanyar tsarin ga-ni-ga-ka ta manhajar Zoom.
 
Ɗimbin jama’a sun mahalarci taron ta hanyar Zoom
Kuma an yi shi ne tare da haɗin gwiwa tsakanin kamfanin shirya finafinai na Moving Image da ke Kano da Tsangayar Aikin Jarida ta Jami’ar Bayero, Kano (BUK).
Farfesan ya ƙara da cewa haɗin kan nasu ba zai tsaya iya shirya wannan taron ba, domin kuwa tsangayar za ta ci gaba da haɗa kai da kamfanin Moving Image, mai shirya taron na shekara-shekara, don ganin an ciyar da harkar shirya finafinai gaba. 
 
A nasa jawabin, shugaban Moving Image kuma jagoran shirya taron, Alhaji Abdulkareem Muhammad, ya bayyana farin cikin sa ganin yadda su ka gabatar da taron a karo na uku cikin kwanciyar hankali tare da samun haɗin kan al’umma, musamman waɗanda su ka halarta.
 
Bugu da ƙari, ya yaba wa Tsangayar  Aikin Jarida ta BUK kan irin gudunmawar da ta bayar wajen ganin an yi taron lafiya ba tare da tangarɗar kayan aiki ba.
 
Wasu mahalarta taron
A yayin taron, an gabatar da maƙaloli kimanin 22 waɗanda su ka fito daga sassa daban-daban na Nijeriya da ƙasar waje.
 
Masu gabatar da maƙalolin sun fito daga Kano, Legas, Abuja, Jamus da sauran su daga jami’o’i, kwalejojin fasaha da na iliimin aikin koyarwa.
 
Sai dai har zuwa lokacin kammala taron, mujallar Fim ba ta ga ‘yan masana’antar shirya finafinan Hausa ta Kannywood a ciki ba duk da irin kiraye-kirayen da aka yi kan su fito su rungumi wannan tsarin domin taimaka wa cigaban sana’ar tasu.
 
Lokacin gudanar da taron
Idan kun tuna, mujallar Fim ta kawo maku tattaunawar da ta yi da Alhaji Abdulkareem Muhammad a game da taron, inda ya bayyana irin ƙalubalen da su ke fuskanta kan shirya taron, musamman ƙin shiga taron da ‘yan Kannywood su ka yi.

Loading

Previous Post

Yadda Mamadou Tandja ya ɓata rawar sa da tsalle a shugabancin Nijar

Next Post

Gwamnan Ondo ya yabi shirye-shiryen rage raɗaɗin rayuwa

Related Posts

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim
Labarai

MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim

June 2, 2025
Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22
Labarai

Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22

May 20, 2025
Hukuma ta rufe gidajen gala a Kano har sai bayan Ramadan
Labarai

Gwamnatin Kano ta dakatar da haska finafinan Kannywood 22 a intanet da talbijin 

May 19, 2025
Labarai

Gwamnan Kano ya ɗauki nauyin ‘yan Kannywood 5 zuwa Hajjin bana

April 17, 2025
Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu
Labarai

Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu

March 28, 2025
Next Post
Sadiya Umar Farouq da Rotimi Akeredolu

Gwamnan Ondo ya yabi shirye-shiryen rage raɗaɗin rayuwa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!