TSOHON Shugaban Masu Shirya Finafinai ta Arewa (AFMAN), Alhaji Hamisu Lamiɗo Iyan-Tama, ya yi kira ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya jingine komai har sai ya magance matsalar tsaro da ta addabi ƙasar nan.
A cikin wata buɗaɗɗiyar wasiƙa da ya wallafa a Facebook, fitaccen jarumin kuma furodusa ya ce wa Tinubu: “Assalamu alaikum ya mai girma Shugaban Ƙasa da al’ummar Nijeriya, Alhaji Bola Ahmad Tinubu. Shawara zuwa ga gwamnatin Nigeriya ta dakatar da duk wani nau’in aiki da ta sa a gaban ta ko wanne iri ne har sai an shawo kan tare da magance matsalar tsaro da ‘yan kidinafin ko da kuwa zai ɗauke ka wata shida ko shekara.
“Sannan kuma a haɗa da magance matsalolin da su ke haifar da hauhawar farashin kayan masarufi da tashin dala. A tsawatar wa da manyan ‘yan kasuwa da manyan kamfanonin wannan ƙasa, a taka masu birki, su na ƙara wa al’ummar ƙasa farashi ba gaira babu dalili. Waɗannan kamfanoni da manyan ‘yan kasuwa sun tsotse jinin talakawan ƙasa sun zo su na san musu kwano 8-8 na shinkafa da taliya.”
Iyan-Tama, wanda shi ma ɗan siyasa ne, ya ci gaba da cewa, “Shugaban Ƙasa ka ke kamar yadda Hukumar Zaɓe ta ayyana kai ka lashe zaɓe. Ina ganin ‘yan Nijeriya su na da haƙƙin ba ka shawara da su ke ganin za ta iya zama alheri ga kai kan ka da ƙasar ka da kuma al’ummar ƙasar.
“A tsaya cak, kowa ya fito a fafata har sai waɗannan abubuwa sun yi wa ƙasa da al’ummar ƙasa daidai tukun, kafin ka ɗora da wasu aikace-aikace don cigaban ƙasa.
“Da yawa yawan abin da ke zuwa kunnen ka ba shi ne ainihin abin da ke faruwa ga al’ummar ƙasar nan ba.
“Allah ya sa wannan saƙo ya isa zuwa gare ka.
“Domin neman ƙarin bayani sai a tuntuɓe ni. Makusantan ka sun san hanyar da za a bi idan buƙatar hakan ta taso.”
Mutanen da su ka karanta wannan buɗaɗɗiyar wasiƙar da dama sun bayyana goyon baya ga abin da ta ƙunsa.