TARON hasalallun gwamnonin PDP biyar masu neman a cire Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Iyorchia Ayu, ya samu tangarɗa.
Taron, wanda aka gudanar a ofishin tsohon mataimakin shugaban PDP na ƙasa, Olabode George, a Ikeja, ya samu halartar dukkan gwamnoni biyar masu adawa da shugabancin Ayu.
Rashin amincewar su da Ayu ne ya kai su ga ƙaurace wa rangadin neman zaɓen shugaban ƙasa da Atiku Abubakar ya fara.
Gwamnonin biyar su ne Nyesom Wike na Jihar Ribas, Samuel Ortom na Binuwai, Seyi Makinde na Oyo, Ifeanyi Ugwuanyi na Inugu da Okezie Ikpeazu na Abiya.
A ranar Litinin ce su ka yi sanarwar kafa ƙungiyar G5, kuma su ka kira ta da ‘Integrity Group’, wadda su ka kafa da niyyar abin da su ka kira “saita PDP kan turbar yin adalci.”
Sai dai kuma wasu gungun magoya bayan Atiku da PDP sun hana taron gwamnonin biyar yin armashi.
A wurin taron, magoya bayan ɗan takarar sun riƙa rera take da kirarin “Atiku! Atiku! Atiku!” da ƙarfi a daidai lokacin da George ya fara bayanin cewa ba za su yi zaɓen shugaban ƙasa da na gwamnonin PDP ba, amma za su yi zaɓen ‘yan Majalisar Dattawa da na Majalisar Wakilai.
Membobin PDP na Jihar Legas sun halarci taron saboda sun gano akwai maƙarƙashiyar da ake zargin Bode George ya shirya domin ya karya lagon Atiku.
Ɗaya daga cikin membobin PDP a Legas mai suna Kunle Folorunsho ya saki wani bidiyo da ke tabbatar da cewa ya halarci taron, kuma akwai hayaniyar da ta kaure wurin taron duk a cikin gajeren bidiyon.
Ya ce yayin da George ya ke cikin bayanin cewa su ba za su zaɓi Atiku ba, nan da nan sai shi kuma ya miƙe tsaye ya ƙalubalance shi da cewa ai PDP ta na da ɗan takarar ta, Atiku Abubakar, kuma shi za su zaɓa.
Folorunsho ya ce tun bai gama rufe baki ba sai magoya bayan George su ka dira kan sa, su ka kekketa masa riga.
Ya ce: “Da ƙyar wasu magoya bayan Atiku su ka cece ni daga hannun magoya bayan Bode George.”
Yayin da gwamnonin ke shirin fita daga ɗakin taron, Folorunsho ya ce dandazon jama’ar da ke waje ba su samu shiga ba sun riƙa rera “sai Atiku, sai Atiku, sai Atiku!”
Hakan da aka yi, a cewar Folorunsho, ya nuna hasalallun gwamnonin biyar ba za su iya raba kan ‘yan PDP a jihar ba.
Gwamnonin G5, tare da sauran hasalallun magoya bayan su, sun shafe sama da awa uku su na tattauna matakin da za su ɗauka a gaba.
Tsohon gwamnan Filato, Jonah Jang, shi ne ya yi magana a madadin sauran gwamnonin, kuma ya ce har yanzu su na kan matsayar da su ka cimma a taron su na Fatakwal, inda su ka ce “ƙofar yin zaman sulhu da mu a buɗe ta ke.”
Sauran waɗanda su ka halarci taron na Legas kuma masu goyon bayan G5 sun haɗa da Sanata Olaka Nwogu, Sanata Ohuabuwa, Sanata Nazifi Suleiman, Bello Adoke, Segun Mimiko, Ayo Fayose, Donald Duke da sauran su.