A YAU Talata, 22 ga Nuwamba, 2022 za a buɗe Bikin Baje-kolin Finafinan Harsunan Afirka na Kano, wato ‘Kano Indigenous Languages of Africa Film Market and Festival’ (KILAF), kashi na 5 a birnin Kano.
Bikin, wanda ake shiryawa a kowace shekara, za a buɗe shi da yamma a Hukumar Raya Al’adun Gargajiya ta Jihar Kano da ke Gidan Ɗanhausa.
Za shafe tsawon kwana biyar ana gudanar da bikin, wato daga yau zuwa ranar 27 ga Nuwamba.
A cikin waɗannan kwanakin za a gudanar da abubuwa da dama da su ka shafi kasuwanci da kuma harkokin cigaban harkar fim a ƙasashen Afirka.
Ana sa ran taron zai samu halartar jama’a daga ƙasashe da dama daga Afirka da Turai.

A lokacin da ya ke yi wa mujallar Fim bayani game da taron na bana, shugaban shirya taron, Malam Abdulkareem Muhammad, ya bayyana cewa: “Duk da yake wannan taron shi ne karo na biyar da mu ka shirya, saboda darrusan da mu ka samu a baya hakan ya sa mu ka samar da abubuwan da su ka bambanta ta hanyar cigaba fiye da na baya.”
Ya ci gaba da cewa, “A wannan shekarar mun samu finafinai daga ƙasashen takwas da su ka shiga gasar kuma wannan shekarar ita ce aka samu finafinai masu yawan da su ka kai sama da tamanin waɗanda su ka fito daga ƙasashen Afirka ta Kudu, Fotugal, Kenya da Amurka, kuma duk an yi su ne da harsunan mu na Afirka.
“Baya ga haka, akwai taron sanin makamar aiki da aka shirya da kuma maƙaloli da za a gabatar a Tsangayar Aikin Jarida da ke B.U.K., kuma masana ne daga manyan jami’o’i na duniya za su gabatar, wasu a wajen, wasu kuma ta allon ga-ni-ga-ka.
“Sannan kuma akwai kallon finafinai da za a yi a sinima da kuma yawon buɗe ido ga baƙin mu da kuma cin abincin gargajiya na Afirka.
“Don haka a tsawon kwanaki biyar ɗin da za a yi duk za a gudanar da abubuwa na ilimi da nishaɗantar da jama’a, wanda kuma a rana ta ƙarshe za a bayyana sunayen finafinan da su ka ci gasar da kuma ba su kyautuka tare da karrama mutanen da su ka bayar da gudunmawa a harkar cigaban harkar fim a nan gida da ma Afirka baki ɗaya.”
Mujallar Fim ta ruwaito cewa taken bikin na bana dai shi ne: “Interrogating Change in African Cultures and Traditions through African Indigenous Language Films,” wato “Bin Bahasin Sauyin Da Ke Wanzuwa Cikin Al’adun Afrika ta Hanyar Finafinan Harsunan Gado na Afrika”.
![]()







Salam,Alhamulillah,da muka kawo wannan Gabar a Harkar Fina finai,musamman na Harshen,Kasashenmu na Afirka.Malam Abdulkareem ku kara zage Dantse,dan ganin Cigaban wannan Masana’anta tamu.Ayi Biki lfy.