INNA lillahi wa inna ilaihi raji’un! Allah ya yi wa mahaifiyar fitaccen jarumin finafinan Hausa, A.S. Muhammed, rasuwa.
Hajiya Hadiza Muhammad ta rasu jiya a Kaduna bayan gajeren rashin lafiya, ta na da shekara ɗari da wata ɗaya.
A.S. Muhammed, wanda ya na daga cikin manyan jaruman Kannywood mazauna Kaduna, ya faɗa wa mujallar Fim cewa mahaifiyar tasa ta rasu ta bar ‘ya’ya huɗu (maza biyu, mata biyu) da kuma jikoki 50.
Jarumin, wanda ma’aikacin hukumar shige-da-fice ne, wato ‘Immigration’, shi ne na uku a cikin ‘ya’yan.
Allah ya jiƙan Hajiya Hadiza, ya saka mata da gidan Aljannar Firdausi, amin.