• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, August 26, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Majalisar Dattawa ta ba Yakubu wa’adi na 2 a shugabancin INEC

by DAGA WAKILIN MU
December 1, 2020
in Nijeriya
0
Majalisar Dattawa ta ba Yakubu wa’adi na 2 a shugabancin INEC
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
A yau Talata ne Majalisar Dattawa ta amince da naɗin Farfesa Mahmood Yakubu a matsayin Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) a karo na biyu.
 
Wannan tabbacin da majalisar ta yi masa ya biyo bayan miƙa rahoton da shugaban Kwamitin Hukumar Zaɓe ta Ƙasa na majalisar, Sanata Kabiru Gaya, ya yi a lokacin zaman majalisar.
 
Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa tun a ranar 25 ga Nuwamba ne Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya aika wa Majalisar Dattawa da sunan Yakubu a matsayin zaɓin sa na Shugaban INEC a karo na biyu bayan wa’adin sa na farko ya ƙare.
 
Lokacin da ya ke miƙa rahoton, Sanata Gaya ya ce a lokacin da ‘yan kwamitin su ke aikin tantance wanda aka zaɓan, sun gano cewa mutum ne wanda zai iya aikin kuma ya dace da wannan sabon naɗin nasa.
 
Ya ce: “Kwamitin ya gano cewa babu wata takardar tuhuma ko rashin amincewa da shi da aka rubuto, kuma ya nuna zurfin sani, sannan mutum ne mai nagartar halayya.”
 
Ya ƙara da cewa tabbatar da sake naɗin an yi shi ne a ƙarƙashin Sashe na 153(1F) na kundin Tsarin Mulki.
 
Yayin da yake sa baki a tattaunawa kan al’amarin, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan, Omo Ovie-Agege, ya ce, “Wannan shi ne karo na farko da aka sake zaɓen Shugaban INEC ya yi wa’adi na biyu a muƙamin sa.
 
“Ya kamata a yaba wa Shugaba Muhammadu Buhari domin ya hango abin da yawancin ‘yan Nijeriya su ka gani wajen yadda Farfesa Yakubu ya riƙa gudanar da al’amuran INEC a tsawon shekaru biyar da su ka gabata.”
 
Ya ce su ma ‘yan kwamitin da su ka bada shawarar a tabbatar wa da Yakubu da wannan naɗi na wa’adi na biyu, sun nuna akwai ƙa’idojin da aka rataya a wuyan INEC a dokar da ta kafa ta, wato Dokar Zaɓe.
 
Ya ce, “Saboda haka, sun kawo muhimman dabaru kan yadda za mu iya kawo gyara a tsarin ta hanyar amincewa da wanda aka zaɓa ɗin.”
 
Shi ma Sanata James Manager (PDP-Delta), ya bayyana wanda aka zaɓa ɗin da cewar mutum ne wanda ya nuna tsantsar bajinta da adalci a wajen gudanar da zaɓuɓɓuka a zamanin wa’adin sa na farko.
 
Ya ce: “Ina kira ga  wanda aka zaɓa ɗin da ya ƙara yin kaffa-kaffa da ma’aikatan INEC. Dalili shi ne sunan da zai yi bayan an ƙara naɗa shi ya fi nasarorin da ya samu a baya.
 
“Ya kamata ya yi aikin domin ya bar baya da kyau, wanda zai fi abin da ya yi a baya muhimmanci.”
 
Sanata Sandy Onor (PDP-Cross River) kuma ya ce Farfesa Yakubu alƙali ne wanda bai nuna wariya, ya ƙara da cewa naɗin da aka yi masa ya dace da shi ƙwarai da gaske. 
 
Ya ce: “Wanda aka zaɓan ya nuna ƙwarewa, kuma ba shakka ya nuna cewa shi alƙali ne wanda ba ya nuna wariya. A yau, ‘yan siyasa ba su shiga zaɓe da fargabar ko za a musguna masu.
 
“Idan mu ka dubi nasarorin sa a wa’adin sa na farko, za mu ga cewar zai ma yi aiki fiye da da a wannan wa’adin na biyu. 
 
“Ina sa ran in ga idan zai maida dukkan al’amurran zaɓen mu su koma ta intanet da komfuta kawai fiye da yadda ya yi.”
 
Ban da Yakubu, a yau ɗin ma Majalisar Dattawan ta amince da naɗin Sanusi Garba a matsayin Shugaban Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Nijeriya (NERC). Haka kuma ta amince da naɗin
Dakta Musiliu Olalekan Oseni a matsayin Mataimakin Shugaban hukumar da kuma Aisha Mahmud  a matsayin Kwamishina a hukumar ta NERC.

Loading

Previous Post

Mustapha Musty: Mun yi soyayyar shekara 13 kafin in auri Soha

Next Post

Bayan neman afuwa, kotu ta sakar wa Naziru Sarkin Waƙa mara

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Naziru Sarkin Waka da takardar sa ta ban-haƙuri

Bayan neman afuwa, kotu ta sakar wa Naziru Sarkin Waƙa mara

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!