• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, June 17, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Mansurah Isah ta yi Allah-ya-isa kan mutuwar auren ta

by DAGA IRO MAMMAN
July 22, 2021
in Labarai
1
Mansurah Isah ta yi Allah-ya-isa kan mutuwar auren ta
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram


“Allah ka saka min. Allah abin da su ke min ka yi musu, ka yi wa yaran su, iyayen su, ‘yan’uwan su. Allah ka jarabce su da ƙuncin rayuwa na aure domin su gane kuskuren su. Amin ya Allah.”


TARE da waɗannan zafafan kalamai, fitacciyar jaruma mai ritaya, Mansurah Isah, a daren yau ta yi Allah-ya-isa ga mutanen da su ke aibanta ta a soshiyal midiya saboda mutuwar auren ta.

Idan kun tuna, a ranar 28 ga Mayu, 2021 mujallar Fim ta ba ku labarin mutuwar auren Mansurah da fitaccen jarumi kuma mawaƙi Sani Musa Danja.

Akwai ‘ya’ya huɗu a tsakanin su – mace ɗaya, maza uku.

Mutuwar auren ta girgiza mutane tare da jawo ka-ce-na-ce a soshiyal midiya, inda mutane su ka dinga tofa albarkacin bakin su.

To ban da masu taya Mansurah alhini, akwai masu zagin ta, ashe ma wasu har ta hanyar saƙon kai-tsaye gare ta ta bayan fage, wato ‘direct message’ ko DM.

A kan masu irin wannan aibanta ta ɗin ne Mansurah ta tura saƙo na musamman a Instagram a yau, inda ta jawo hankalin su ga munin abin da su ke aikata mata.

A cewar ta, ɓatancin da su ke yi mata ya na taɓa rayuwar ta ta hanyar da ba su zato.

A saƙon mai shigen fosta, wanda ta yi da salon ingausar Hausa da Turanci, wanda kuma mujallar Fim ta fassara, Mansurah ta fara da cewa ta lura da yadda duk motsin da ta yi a soshiyal midiya tun bayan mutuwar auren ta sai wasu ‘yan sa ido sun soke ta a kai. “Yara, har da tsofaffi fa, har DM su na zagi na,” inji ta.

Kafin ta wallafa saƙon ta na Allah-ya-isa, sai da Mansurah Isah ta bada sanarwar ta na rubuta wani saƙo da za ta tura

Ta ce: “Na yi hoton Sallah, kun ce abin da ya sa na fito kenan. Na yi tafiya zuwa wani gari, kun ce shi ya sa na kashe aure na. Na je cin abinci da ƙawaye na, kun ce iskancin da na ke son yi kenan. Na je aikin NGO na rabo da na saba yi yau wajen shekara 20 kenan ina yi, kun ce da man yawon da ya fito da ni kenan.”

Ta ce akwai masoyan ta waɗanda za su so ta yi haƙuri kada ta tanka wa irin waɗannan mutanen, to amma fa rayuwar ta ce ake taɓawa kuma ta na da ‘yancin ta yi abin da ta ga damar yi da rayuwar ta. 

Ta tambaye su da cewa shin kalmar “saki” ce “ba ku taɓa ji ba ne, ko kuma ba ku taɓa ganin mace da aka saka ba?”

Da ta dubi batun mutuwar auren nata ta fuskar addini kuma, sai ta faɗa wa masu kushe ta cewa, “Annabin tsira (SAW) ya taɓa sakin mace. Allah da ya halicce mu ya halasta (saki). 

“Me ku ke so a matsayin mu na muminai da bin dokokin Allah? Umarnin ku za a bi ko na Allah?”

Ta ƙara da cewa, “Ni dai na san ban yi wa kowa laifi ba. Wasu har da buɗe sabon ‘account’ don su zage ni. Haka nan kawai.”

Tsohuwar jarumar kuma shugabar ƙungiyar agaji ta ‘Today’s Life Foundation’ ta ce in dai batun saki ne, ai ba kan ta farau ba. “Ba ni kaɗai ba ce mace mai aure ko wacce aka saka a soshiyal midiya’ ba.”

Bugu da ƙari, ta yi nuni da yadda mutane ‘yan sa ido ba su cewa uffan kan ‘ya’ya mata da ake gani cikin shigar rashin mutunci a soshiyal midiya, sai ‘yan fim kaɗai ake wa kwakwazo. Ta ce da su, “In kun ga yaran masu kuɗi tsirara ba ɗankwali a kan su, ko su na abin da su ka ga dama a soshiyal midiya, ku yabe su, in ‘yar fim ta yi daidai irin wannan ɗin ku zage su. Kun yi wa kan ku adalci kenan? Ku ji tsoron Allah wallahi.”

Saƙon da Mansurah Isah ta wallafa a Instagram

Mansurah ta yi kira ga masu sukar ta ɗin da su dubi kan su tukuna kafin su yanke mata hukunci. Ta ce, “In kun koma gida ku tambayi ‘yan’uwan ku mata, ko uwayen ku ko maƙwabtan ku da aka taɓa saka, su faɗa maku yadda su ke ji, ku tambaye su faman da su ke yi da rayuwa. Su ba ku amsa, sannan ne za ku san abin da ku ka yi mani.” 

Haka kuma Mansurah Isah ta yi rantsuwar ba za ta yafe wa duk wani wanda ya zage ta ko ya aibanta ta ba.

Cikin kausasan kalamai, ta ce: “Ba zan taɓa yafe wa duk wani wanda ya musguna wa rayuwa ta ba. Allah ya isa. Allah ka saka min.”

A ƙarshe, Mansurah ta roƙi Allah da ya bi mata haƙƙin ta a kan su. Ta ce: “Allah abin da su ke min ka yi musu, ka yi wa yaran su, iyayen su, ‘yan’uwan su. Allah ka jarabce su da ƙuncin rayuwa na aure domin su gane kuskuren su. Amin ya Allah. Amin don wata mai albarka da mu ke ciki. Amin ya Allah.”

Wannan dai shi ne karo na farko da Mansurah ta fito ɓaro-ɓaro ta yi magana kan mutuwar auren ta tun bayan sanarwar farko da ta wallafa inda ta bada sanarwar tsinkewar igiyar auren.

Shigar ranar Sallah ta Mansurah Isah

Loading

Tags: divorceFim MagazineKannywoodMansurah IsahSani Musa DanjaSocial mediasoshiyal midiyaToday's Life Foundation
Previous Post

Hotunan ‘yan fim a ranar Babbar Sallah

Next Post

Ɓarayin da su ka sace jagoran harkar fim a Zamfara, Ali Bulala Gusau, na neman diyyar naira miliyan 30

Related Posts

Furodusan Kannywood, Abubakar Galadima ya zama jakaden garin sinadarin girki na Zahir Spice Curry
Labarai

Furodusan Kannywood, Abubakar Galadima ya zama jakaden garin sinadarin girki na Zahir Spice Curry

June 15, 2025
Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
Next Post
Ɓarayin da su ka sace jagoran harkar fim a Zamfara, Ali Bulala Gusau, na neman diyyar naira miliyan 30

Ɓarayin da su ka sace jagoran harkar fim a Zamfara, Ali Bulala Gusau, na neman diyyar naira miliyan 30

Comments 1

  1. Bashir Mudi Yakasai says:
    4 years ago

    Comment:l

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!