HAƊAƊƊIYAR Ƙungiyar Marubuta ta Jihar Katsina ta yi gagarumin bikin rantsar da sababbin shugabannin ta.
An yi bikin a ɗakin taro na Ƙungiyar Ma’aikatan Lafiya ta Jihar Katsina da ke cikin birnin Katsina a ranar Asabar, 30 ga Yuli, 2023.
Barista Aliyu Isah ne ya rantsar da sababbin shugabannin tare da miƙa masu takardar shaidar lashe zaɓe.

Shugabannin su 11, waɗanda aka zaɓa tun a ranar 1 ga Yuli, 2023, su ne:
Abubakar Almustapha Yar’Adua – Shugaba; Fatima Hussaini El-Ladan – Mataimakiyar Shugaba; Musa Mairafi – Magatakarda; Maryam Nuhu Turau – Mataimakiyar Magatakarda; Fatima Saminu – Ma’aji; Salisu Muhammad Arabi – Sakataren Tsare-tsare, da Khadija Hidaya
Mataimakiyar Sakataren Tsare-tsare.

Sauran su ne Usman Ya’u Ango – PRO na 1; Rabi’atu SK Mashi – PRO ta 2; Isa Sani Randawa – Mai Binciken Kuɗi, da A’isha Muhammad Sabitu (Mobil) – Sakatariyar Walwala da Jin Daɗi.
Taron ya samu halartar manyan baƙi irin su wakilin mai girma Magajin Garin Katsina da Injiniya Surajo Yazid Abukur da Injiniya Muttaqha Rabe Darma.




![]()






