• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 30, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano

by MUKHTAR YAKUBU
June 20, 2025
in Labarai
0
Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano

Dakta Korao Hamadou yana gabatar da maƙalar sa a taron

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

WANI masanin harshen Hausa ɗan ƙasar Nijar Dakta Korao Hamadou ya gabatar da waɗansu haruffa a Kano waɗanda ya ce su ne baƙaƙen rubutun Hausa na asali tun kafin zuwan rubutun ajami ko abacada na Turawa.

Ya gabatar da su ɗin ne a maƙalar da ya gabatar a wurin wani taron wuni guda da aka gudanar da a ɗakin taro na CBN Centre da ke cikin sabuwar Jami’ar Bayero da ke Kano.

A taron, wanda ya samu halartar manyan malamai da masana a kan harshen Hausa daga sassa daban-daban na duniya, Dakta Hamadou ne babban baƙo mai jawabi.

Ya ce sababbin haruffan “an samo alamomin su ne daga masu bayar da magungunan gargajiya ta hanyar taskace sassaƙe da saiwoyi da ganyaye da kauci da kuma ɓawo.”

Malamin ya gabatar da waɗannan alamomi a gaban manyan malaman harshen Hausa, inda ya kafa hujja da cewa irin waɗannan alamomi su ne na farko a wajen samar da rubutu a duniya.

Masanin ya kawo sunayen manyan litattafan tarihi da na Musulunci da suke nuna cewa lallai Hausawa ne suka fara samar da wani abin rubutawa da irin waɗannan alamomi.

Haka kuma ya kawo misalai da dama a kan yadda za a yi amfani da haruffan da yadda za su bunƙasa idan ana amfani da su.

Mahalartan taron suna sauraren Dakta Hamadou

Manyan malaman Hausa da na Tarihi sun tafka muhawara a kan waɗannan alamomi.

Ɗaya daga cikin su, Farfesa Hafizu Miko Yakasai, ya ƙalubalanci Dakta Ahmadu a kan haruffan ta yadda ba su samu sahalewar manyan malaman Hausa ta hanyar gabatar da su ba.

Ya ce idan ta hanyar masu bada magani ko itatuwa da kauci da ganye aka same su, to ai akwai tsofaffin hanyoyi na sana’o’i irin su ƙira, fawa, da dukanci, to su kuma ina irin nasu yake?

An shafe tsawon lokaci ana yi masa tambayoyi, yayin da shi kuma a dunƙule ya bada amsa da cewar wannan wani ɓangare ne na ilimi mai zurfi da haruffan suke ɗauke da shi, kuma ilimi sirri ne da shi don haka bai kamata ya bayyana shi ba tun kafin lokacin ƙaddamar da shi ba.

Ya ce a jira lokacin da za a ƙaddamar da shi, saboda akwai sauran nazari da bincike da yake yi kafin ya saki ilimin ga al’ummar duniya.

Ana sa ran nan gaba za a yi wani taron masana ilimin kimiyyar harshe da masana tarihi da al’adu domin samar da matsaya a kan waɗannan alamomi.

Mahalartan taron

Hotunan Rubutun Hausa na Asali Da Dakta Korao Hamadou Ya Kawo a Taron

Haruffan Hausa na asali da Dakta Hamadou ya bayyana

Loading

Previous Post

Ministan Yaɗa Labarai ya yaba wa Hafsoshin Soji kan cigaban da aka samu a fannin tsaron ƙasa a shekaru biyu

Next Post

Kiran Gwamnatin Tarayya ga ‘yan jarida: Ku zama jigo wajen gina dimokiraɗiyyar Nijeriya

Related Posts

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

June 22, 2025
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau
Labarai

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

June 22, 2025
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

June 22, 2025
Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza
Labarai

Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza

June 20, 2025
Kotu a Kano ta ɗaure ɗan TikTok Abubakar Kilina shekara ɗaya ko zaɓin tara
Labarai

Kotu a Kano ta ɗaure ɗan TikTok Abubakar Kilina shekara ɗaya ko zaɓin tara

June 19, 2025
Next Post
Kiran Gwamnatin Tarayya ga ‘yan jarida: Ku zama jigo wajen gina dimokiraɗiyyar Nijeriya

Kiran Gwamnatin Tarayya ga ‘yan jarida: Ku zama jigo wajen gina dimokiraɗiyyar Nijeriya

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!