• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, May 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Mawallafin jaridun Manhaja da Blueprint, Mohammed Idris Malagi, ya yi alhinin rasuwar Janar Wushishi

by DAGA IRO MAMMAN
December 6, 2021
in Nijeriya
0
Marigayi Janar Mohammed Inuwa Wushishi

Marigayi Janar Mohammed Inuwa Wushishi

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

SHUGABAN kamfanin buga jaridun Blueprint da Manhaja, Alhaji Mohammed Idris Malagi, ya miƙa saƙon ta’aziyya ga ɗaukacin ‘yan Nijeriya dangane da rasuwar tsohon Hafsan Hafsoshin Soja, Janar Mohammed Inuwa Wushishi.

Alhaji Mohammed, wanda shi ne Kakakin Nupe, ya miƙa saƙon ta’aziyyar tasa musamman ga Gwamnan Jihar Neja, Alhaji Abubakar Sani-Bello, da ɗaukacin al’ummar Wushishi, Masarautar Kwantagora, jama’ar jihar, da Rundunar Sojojin Nijeriya a kan rasuwar ta Janar Wushishi, wanda ya riƙe muƙamin Hafsan Hafsoshin Sojan Nijeriya a tsakanin Oktoba 1981 zuwa Oktoba 1983.

A saƙon ta’aziyyar da ya aika a ranar Lahadi, Alhaji Mohammed Malagi ya bayyana mamacin a matsayin dattijon kirki wanda ya yi amfani da aikin sojan da ya yi cikin martaba da kuma hikimomin sa na kasuwanci ya ƙarfafa wa ‘yan Nijeriya daban-daban gwiwa wajen neman na kan su.

Ya ce, “Janar Wushishi ya na daga cikin manyan hafsoshin soja da su ka yi yaƙi domin tabbatar da haɗin kan Nijeriya, kuma ya tsaya tsayin daka a kan wannan ƙudirin na ganin haɗin kan ƙasa da dunƙulewar jama’a a duk tsawon rayuwar sa.

“Abu ne mai wahala a ce mu da mu ke a wannan zamanin ba mu amfana daga koyon halaye nagari irin na Janar Wushishi da sa’o’in sa ba wajen ciyar da batun haɗin kan Nijeriya ta zama ƙasa ɗaya.”

Mawallafin jaridun, wanda kuma shi ne shugaban gidan rediyon ‘We FM’ da ke Abuja, ya ƙara da cewa ya yi alhini matuƙa kan wannan rashi da aka yi, to amma ya karɓi ƙaddara musamman ganin cewa Janar Wushishi ya bar ababen da miliyoyin ‘yan Nijeriya za su ci gaba da koyi da su har abada.

Alhaji Mohammed Idris Malagi ya roƙi Allah subhanahu wa ta’ala da ya yafe dukkan kurakuran mamacin kuma ya yi masa sakayya da gidan Aljannar Firdausi.

Haka kuma ya ba al’ummar Wushishi da Masarautar Kwantagora da jama’ar Neja da Rundunar Sojojin Nijeriya da ma ɗaukacin ‘yan Nijeriya haƙurin jure wannan babban rashi.

Shi dai Janar Wushishi, Allah ya yi masa rasuwa ne a ranar Asabar, 4 ga Disamba, 2021, a wani asibiti da ke birnin London. 

Ya rasu ya na da shekara 81 kuma ya bar matar sa ɗaya, Hajiya Kande Inuwa Wushishi, da ‘ya’yan su guda bakwai.

Loading

Tags: Abubakar Sani-BelloBlueprint newspapersJanar Mohammed Inuwa WushishiManhajaMohammed Idris MalagiNiger StaterasuwaWe FM
Previous Post

Aure da Sani Danja: Ni kaɗai na san wahalar da na sha, inji Mansurah Isah

Next Post

Abdul D. One: Yadda na haɗu da Ummu-Salma da zan aura

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Abdul D. One tare da 'Favourite', Ummu-Salma Sulaiman

Abdul D. One: Yadda na haɗu da Ummu-Salma da zan aura

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!