• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, August 23, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Abdul D. One: Yadda na haɗu da Ummu-Salma da zan aura

by DAGA ABBA MUHAMMAD
December 7, 2021
in Ranar Murna
1
Abdul D. One tare da 'Favourite', Ummu-Salma Sulaiman

Abdul D. One tare da 'Favourite', Ummu-Salma Sulaiman

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

FITACCEN mawaƙi a Kannywood, Abdulƙadir Tajuddeen, wanda aka fi sani da Abdul D. One, ya bayyana yadda ya fuskanci wata matsala wadda ta kusa yin barazana ga yiwuwar auren sa da yarinyar da zai aura nan da kwanaki biyar masu zuwa.

Za a ɗaura auren Abdul da Ummu-Salma Sulaiman, wadda ake kira ‘Salma Fresh’, da misalin ƙarfe 11 na safe a ranar Lahadi, 12 ga Disamba, 2021 a Kwanar ‘Yan Gana Bus Stop, Layin Transformer, a unguwar Tudun Murtala cikin birnin Kano.

Tun a makon jiya aka fara yaɗa hotunan kafin aure na mawaƙin da sahibar tasa, ana yi masu addu’o’i da fatan alheri.

A yayin da ya ke yi wa mujallar Fim bayani kan yadda ya haɗu da Ummu-Salma, Abdul ya ce, “Mata ta dai ko sahiba kamar yadda ka ambata, amma ni ina ce mata ‘Favourite’, na haɗu da ita a wata unguwa da ake kira Tudun Murtala, sannan kuma ina tare da ita tun shekarar 2019.”

Da yake kusan ko wane neman aure ya kan zo da wata mishkila, wakilin mu ya tambayi angon irin ƙalubalen da shi ya fuskanta wurin neman wannan auren, musamman a matsayin sa na mawaƙi. 

Sai ya amsa da cewa, “Na samu ƙalubale sosai, domin tun ranar da mu ka fara haɗuwa da ita, mun samu matsala da yayyen ta. To tun wannan haɗuwar ta farko ba mu ƙara haɗuwa da ita ba, don ba daga haɗuwa ta farko da mutum za ka nuna ka na son shi ba, da sauran su.

“Kuma ko a lokacin da na haɗu da ita da ma ‘fan’ ɗi na ce gaskiya sosai. Don a daidai lokacin mun saki waƙar ‘Kar Ki Manta Da Ni’, to da ma dai ta na bibiyar waƙoƙi na kowane lokaci, sai Allah ya haɗa mu a wurin wani taro.

Ummu-Salma da Abdul: Sauran kwana biyar su zama mallakin juna

“Wata rana ba ta da lafiya, ni kuma a daidai lokacin na je Kano, da ma kwana biyu ba na ganin ta ‘online’, sai na ke tambayar ta me ya same ta? Sai ta ce mani ba ta da lafiya ne. Sai na je duba ta. 

“A wurin dubiyar da na je, mun samu matsala da yayyen ta maza, shi ma kuma wannan rashin fahimta ne. Amma daga baya da su ka fahimce ni, sai komai ya yi daidai.”

A ƙarshe, mujallar Fim ta tambayi Abdul D. One abin da zai ce game da wannan aure da zai yi, shi kuma ya amsa da cewa, “Alhamdu lillah! Abin da zan ce ina farin ciki sosai, saboda zan auri abin da na ke so ne, kuma ta ke so na. 

“Ina farin ciki sosai. Na daɗe ban samu farin ciki irin wannan ba.”

Shi dai Abdul D. One, ɗan asalin garin Dukke ne da ke yankin Ƙaramar Hukumar Funtuwa a Jihar Katsina.

Ya na daga cikin yaran fitaccen mawaƙi kuma jarumi Umar M. Shareef. 

Ya samu nasibin waƙa cikin ƙanƙanen lokaci a ‘Shareef Studio’. Yanzu kuma shi ne shugaban ‘AD Music Studio’.

Kamar yadda mu ka taɓa ba ku labari, Abdul, wanda mazaunin Kaduna ne, matashin mawaƙi ne mai farin jini, wanda ya sa ya yi soyayya da ‘yan mata daban-daban.

‘Kar ki manta da ni’, ‘Kar ka manta da ni’: Salma Fresh da Abdul su na yi wa juna kallon ƙuda

Soyayyar sa da jarumar Kannywood ɗin nan Sa’adatou Abubakar Marana, ‘yar ƙasar Nijar, ita ta fi jan hankali, amma auren su bai yiwu ba, su ka ƙare da musayar baƙaƙen maganganu saboda kowannen su ya zargi ɗayan da yaudarar ɗayan. 

Daf da azumin Ramadan da ya gabata, Sa’adatou, wadda ke zaune a Yamai yanzu, ta bayyana cewa ta yi aure.

Yanzu dai Ummu-Salma ce matar da Allah ya ba Abdul. Da ma Hausawa sun ce matar mutum kabarin sa.

Cewar Abdul D. One, “Na daɗe ban samu farin ciki irin wannan ba”
Katin gayyatar zuwa ɗaurin auren Abdulƙadir Tajuddeen da Ummu-Salma Sulaiman

Loading

Tags: Abdul D. Oneaurehausa filmsHausa musicKannywoodSaadatou MaranaTudun MurtalaUmar M. ShareefUmmu-Salma Sulaiman
Previous Post

Mawallafin jaridun Manhaja da Blueprint, Mohammed Idris Malagi, ya yi alhinin rasuwar Janar Wushishi

Next Post

‘Yan bindiga sun harbe jarumar fim har lahira

Related Posts

An ɗaura auren mawaƙi Kawu Ɗan Sarki
Ranar Murna

An ɗaura auren mawaƙi Kawu Ɗan Sarki

August 23, 2026
Uwargida na ce ta biya sadakin aure na da amarya ta – darakta Aminu Saira
Ranar Murna

Uwargida na ce ta biya sadakin aure na da amarya ta – darakta Aminu Saira

August 2, 2026
Bikin auren darakta Aminu Saira a Azare ya ja hankalin jama’a
Ranar Murna

Bikin auren darakta Aminu Saira a Azare ya ja hankalin jama’a

July 31, 2026
An taya Aisar, jikar marubuciya Sadiya Garba Yakasai, murnar cika shekaru 5
Ranar Murna

An taya Aisar, jikar marubuciya Sadiya Garba Yakasai, murnar cika shekaru 5

July 15, 2026
Jarumin Kannywood Tijjani Faraga ya aurar da ‘yar sa ta biyu
Ranar Murna

Jarumin Kannywood Tijjani Faraga ya aurar da ‘yar sa ta biyu

July 12, 2026
Mawaƙi Sa’eed Ja’afar ya samu ƙaruwa da ‘ya mace
Ranar Murna

Mawaƙi Sa’eed Ja’afar ya samu ƙaruwa da ‘ya mace

July 6, 2026
Next Post
Ngozi Chiemeke

'Yan bindiga sun harbe jarumar fim har lahira

Comments 1

  1. Pingback: Mawaki Abdul D one ya bayyana yadda ya hadu da Ummu-Salma Matar da zai Aura – Kaitatunes.com.ng

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!