• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, August 26, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Minista Alake na cimma nasarori wajen sauya fasalin sashen ma’adinai, inji Idris

Mu abokai ne a fagen siyasa tun tuni, inji Alake

by DAGA IRO MAMMAN
November 24, 2023
in Nijeriya
0
Minista Alake na cimma nasarori wajen sauya fasalin sashen ma’adinai, inji Idris

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris (a dama), tare da Ministan Ma'adinai, Mista Henry Dele Alake, wanda ya kai wa ziyarar aiki a ranar Alhamis a Abuja

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris (a dama), tare da Ministan Ma’adinai, Mista Henry Dele Alake, wanda ya kai wa ziyarar aiki a ranar Alhamis a Abuja

MINISTAN Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yaba wa takwaran sa na Ma’adinai kan abin da ya kira “manyan matakan cigaba da ake samu a Ma’aikatar Ma’adinai da ake ɗauka don kawo sauyi a fagen a matsayin sa na wanda ke sahun gaba na muradun tattalin arzikin Nijeriya.”

A cikin wata sanarwa, Malam Rabi’u Ibrahim, wato mataimaki na musamman ga ministan kan harkokin yaɗa labarai, ya ce Idris ya faɗi haka ne a lokacin da ya kai ziyarar aiki ga Ministan Ma’adinai, Mista Henry Dele Alake, a ranar Alhamis a Abuja.

Ministan ya yi la’akari cikin gamsuwa da cewa ayyuka masu tasiri a fagen ma’adinai waɗanda ke bada sakamako a kyakkyawan sauye-sauye da ake matuƙar buƙatar su da canza muradu, wanda ya yi daidai da manyan manufofin Renewed Hope Agenda ta gwamnatin Tinubu.

A cewar Idris, Mista Alake ya na dasa ginshiƙan gudanarwa waɗanda ba a saba ganin irin su ba a sashen ma’adinai sannan su na haifar da kyakkyawar fata a zuciyar ‘yan Nijeriya game da gina ƙasa mai ƙarfin tattalin arziki.

Ya bayyana ziyarar tasa ga Alake a matsayin ziyarar aiki ta farko da ya kai wa wani takwaran sa minista, ya na faɗin cewa Alake mutum ne wanda ya samu sani daga sassa daban-daban, kuma mai basirar cimma nasara a wani sashe da ya kusa durƙushewa, wanda zai ƙarfafa hanyoyin kuɗin shiga na Nijeriya ya kuma faɗaɗa damar ɗaukar ma’aikata.

Shi kuma Mista Alake sai ya ce shi da Idris sun daɗe su na hulɗar siyasa tare, kuma Idris mutum ne wanda ya yi amanna da ƙudirorin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, musamman wajen abin da ya dace da tattalin arziki da zamantakewar Nijeriya baki ɗaya, ta hanyar Renewed Hope Agenda.

Ya ce: “Idris da ni abokai ne kuma wannan ziyarar ta na alamta burin mu na ciyar da ƙasar nan gaba domin ta zama mai faɗaɗan hanyoyin tattalin arziki kuma mu jawo hankalin duniya zuwa ga sashen ma’adinai a matsayin hanyar jawo wa Nijeriya Jari Kai-tsaye daga Waje, wato ‘Foreign Direct Investment’ (FDI).”

Loading

Tags: Bola Ahmed TinubuDele Alakema'adinaiMohammed IdrisRenewed Hope Agenda
Previous Post

KILAF 2023 rana ta 3: An yi jawabai da bada darussa kan harkar fim

Next Post

Editan finafinai, Hafiz SB ya zama angon Iƙilima

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Editan finafinai, Hafiz SB ya zama angon Iƙilima

Editan finafinai, Hafiz SB ya zama angon Iƙilima

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!