HAƊAƊƊIYAR ƙungiyar masu shirya finafinai ta Kannywood (MOPPAN) ta ƙaddamar da sayar da takardar neman shugabancin ƙungiyar a matakai daban-daban.
Shugaban kwamitin shirya zaɓen, Malam Ahmad Salihu Alkanawy, da sakataren kwamitin, Dakta Ahmad Salihu Bello, sun faɗa a wata takarda da su ka rattaba wa hannu cewa duk mai neman zama Shugaban ƙungiyar dole sai ya cika sharuɗɗa kamar haka:
1. Ya zamana ya na da ƙwarewa a cikin industiri ta tsawon shekara goma.
2. Ya zamana ya samu shaidar kirki.
3. Ya zamana ba shi da wata shaida ta almubazzaranci a sha’anin kuɗi.
4. Ya zamana ba shi da wata tuhuma da ta shafi cin ta’addanci.
5. Ya zamana ya na da duk wata nagarta ta shugabanci a matakin ƙasa.
6. Sai ya biya kuɗin takardar tsayawa takara.
Wanda zai tsaya takarar Mataimakin Shugaba na 1 zuwa na 3 dole ya bi ƙa’idojin da aka gindaya wa ɗan takarar zama Shugaba.
Shi ma mai neman kujerar Sakatare dole ya cika irin ƙa’dojin da mai neman Shugaba ya cika.
Mai neman kujerar Ma’aji kuwa, dole ya cika ƙa’idoji kamar haka:
1. Ya zamana ya na da ƙwarewa a cikin industiri ta tsawon shekara biyar.
2. Ya zamana ya samu shaidar kirki.
3. Ya zamana bai da wata shaida ta almubazzaranci a sha’anin kuɗi.
4. Ya zamana ba shi da wata tuhuma da ta shafi ta’addanci.
5. Ya zamana ya na da duk wata nagarta ta zama Ma’aji a matakin ƙasa.
6. Dole ya biya kuɗin takardar tsayawa takara.
Ƙa’idojin sauran kujerun su ne:
1. Ɗan takara ya zamana ya na da ƙwarewa a cikin industiri ta tsawon shekara biyar.
2. Ya zamana ya samu shaidar kirki.
3. Ya zamana ba shi da wata shaida ta almubazzaranci a sha’anin kuɗi.
4. Ya zamana ba shi da wata tuhuma da ta shafi ta’addanci.
5. Ya zamana ya na da duk wata nagarta a kujerar da ya nema.
6. Dole ya biya kuɗin takardar tsayawa takara.
Shugabannin kwamitin sun kuma bayyana cewa dole ne duk mai neman shugabancin wannan ƙungiya da mataimakan sa su fito daga shiyyoyin ƙasar nan uku kamar haka:
1. Mataimakin Shugaba na 1 – Arewa-maso-gabas.
2. Mataimakin Shugaba na 2 – Arewa ta Tsakiya.
3. Mataimakin Shugaba na 3 – Arewa-maso-yamma.
Haka kuma ana so masu neman waɗannan muƙamai su ɗauki hotunan takardar izinin shiga zaɓen su tura wa wannan imel: sardaunanfce@gmail.com.
Bugu da ƙari, sanarwar ta ce dukkan ‘yan takara za su hallara a gaban kwamitin zaɓe domin a tantance su a ranar jajibirin zaɓen.

Haka kuma dole ne ‘yan takarar su zo da ainihin takardar shiga takarar da kuma shaidar biyan kuɗi ta banki domin tabbatarwa.
Sannan dole kowa ya gabatar da katin shaidar sa.
A ƙarshe, dukkan wanda aka wakilta dole ne ya zo da shaidar kati.
Bugu da ƙari, an bayyana farashin fom-fom na tsayawa takarar kowane muƙami kamar haka:
i. Shugaba – N50,000
ii. Mataimakin Shugaba na 1 zuwa na 3 – N40,000
iii. Sakatare – N40,000
iv. Ma’aji – N30,000
v. Sakataren Kuɗi – N30,000
vi. Mataimakin Sakatare – N30,000
vii. Kakaki – N30,000
viii. Mai Binciken Kuɗi N30,000
ix. Mai Binciken Kuɗi – N30,000
x. Mataimakin Sakatare – N30,000
xi. Mai Kula da Walwala (mace kawai) – N30,000
An bayyana cewa duk wanda zai sayi fom, to ya tura kuɗin zuwa asusun banki kamar haka:
Mohammed Ibrahim Gumel, Access Bank, No. 0040001335.