• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 30, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Mutuwar Samanja babbar asara ce ga ƙasa, inji Tinubu

by DAGA IRO MAMMAN
November 14, 2023
in Labarai
0
Marigayi Alhaji Usman Baba Pategi (Samanja)

Marigayi Alhaji Usman Baba Pategi (Samanja)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

SHUGABA Bola Ahmed Tinubu ya bayyana mutuwar shahararren ɗan wasan kwaikwayo ɗin nan Alhaji Usman Baba Pategi (Samanja) a matsayin babban rashi ga ƙasar nan, saboda ɗimbin gudunmawar sa ga cigaban ta.

Mujallar Fim ta ba ku labarin cewa Samanja, wanda tsohon soja ne kuma ma’aikacin gidan Rediyon Tarayya na Kaduna, ya rasu ne a shekaranjiya Lahadi, ya na da shekaru 84 a duniya.

A saƙon da ya aika wa iyalan mamacin a yau, wanda aka raba wa manema labarai, Tinubu ya yi masu ta’aziyyar wannan babban rashi da aka yi.

A saƙon, wanda mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan yaɗa labarai, Cif Ajuri Ngelale, ya rattaba wa hannu, Tinubu ya bayyana rasuwar a matsayin wani al’amari mai ƙona rai, ya ce marigayin ya bada gudunmawa ga ƙasar nan ta hanyar abubuwa daban-daban da ya yi a rayuwar sa.

Tinubu ya ce: “Marigayi Pategi ya zaɓi ya taimaka wa ƙasa ne a daidai lokacin da ƙasar ke buƙatar sa. Shirin sa na ‘Samanja’ ya wajabta ga kowa a matsayin abin kallo don samun nishaɗi a tsawon shekaru masu yawa.

“Ta hanyar shirin, ya koyar da matasa tarbiyyar son ƙasa tare da girmamawa ga sojojin mu. Mutum ne ɗan kishin ƙasa wanda ya bar ɗimbin abubuwan da za a riƙa tunawa da shi.”

Shugaban ƙasar ya hori iyalan Samanja da al’umma da gwamnatin Jihar Kwara da Majalisar Masarautar Pategi da dukkan masu harkar nishaɗantarwa na Nijeriya da su yi la’akari da abin farin cikin da marigayin ya bari na ayyukan sa abin yabo.

Loading

Previous Post

Hukumar Tace Finafinai ta yi martani kan samamen da Hisbar Kano ke yi a gidajen gala

Next Post

Ban taɓa ganin irin wannan karramawar da aka yi min ba, inji Rikadawa

Related Posts

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

June 22, 2025
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau
Labarai

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

June 22, 2025
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

June 22, 2025
Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano
Labarai

Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano

June 20, 2025
Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza
Labarai

Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza

June 20, 2025
Next Post
Rikadawa riƙe da kambin karramawar sa

Ban taɓa ganin irin wannan karramawar da aka yi min ba, inji Rikadawa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!