AN wayi gari a yau da baƙin labarin rasuwar Malam Nura Mustapha Waye, daraktan fitaccen shirin nan mai dogon zango mai suna ‘Izzar So’.
Nura ya rasu ne a safiyar yau Lahadi, 3 ga Yuli, 2022, da misalin ƙarfe 8:00 na safe a wani asibiti a Kano.
An yi jana’izar sa da misalin ƙarfe 11:00 na safe a gidan sa da ke unguwar Goron Dutse, Kano.
‘Yan fim da mutanen gari sun halarci jana’izar, inda wurin ya cika maƙil babu masaka tsinke.
Wata majiya ta kusa da iyalin marigayin ta shaida wa mujallar Fim cewa daraktan, ɗan kimanin shekara 43, ya rasu ya bar mahaifiyar sa da matar sa da ‘ya’ya 15. A cikin ‘ya’yan, 11 ne nasa, huɗu kuma na wan sa da ya rasu ne, shi kuma ya ɗauko su ya haɗa su da ‘ya’yan sa.

Labarin rasuwar Malam Nura ya kaɗa hantar mutane da dama, musamman ‘yan fim, ba kamar da yake mutuwar ta bazata ce.
Wasu ‘yan fim sun shaida wa mujallar Fim cewa ko a jiya-jiyan nan su na tare da daraktan, kuma babu alamar cewa ba shi da lafiya.
Babban furodusa kuma jarumin ‘Izzar So’, Lawan Ahmad, ya na daga cikin waɗanda su ka fara ba da sanarwar rasuwar, inda ya rubuta haka a Instagram: “Inna lillahi wa inna ilaihir raji’un! Allah ya karɓi rayuwar Nura Mustapha Waye, director Izzar So. Za a yi zana’idar shi ƙarfe 11 na safen nan a gidan sa Goron Dutse Primary in-sha Allah. Allah ya yafe masa kurakuran sa, amin. Allah ya sa idan tamu ta zo mu cika da imani, amin.”
Ali Nuhu kuma ya ce: “Inna lillahi wa inna ilaihir raji’un! Allah ya jarabce mu da babban rashi. Allah ya jiƙan ka Nura, ya kyautata makwanci. Allah ya sa Annabi ya karɓi baƙuncin ka. Jiya war haka mu na tare, ana ta raha. Allah ya jiƙan ka da rahama.”
Sauran ‘yan fim maza da mata, babba da yaro, sun ci gaba da yi wa marigayin addu’ar samun rahama. Da yawan su sun wallafa hotunan sa da bidiyoyin sa inda ya ke bayyana shauƙin soyayyar sa ga Manzon Allah (s.a.w.).

A soshiyal midiya a yau ko’ina ka leƙa maganar rasuwar Nura ake yi da kuma bayyana kyawawan halayen sa da irin soyayyar da ya ke yi wa Annabi Muhammadu (s.a.w.).
Allah ya rahamshe shi, amin.