• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, August 25, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Sadiya Umar Farouq Bazamfariyar ƙwarai ce – Gwamna Matawalle

by DAGA WAKILIN MU
September 27, 2022
in Nijeriya
0
Hajiya Sadiya Umar Farouq tare da Gwamna Matawalle da masu cin moriyar shirye-shiryen a lokacin taron

Hajiya Sadiya Umar Farouq tare da Gwamna Matawalle da masu cin moriyar shirye-shiryen a lokacin taron

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

GWAMNA Bello Muhammed Matawalle na Jihar Zamfara ya bayyana Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, a matsayin nagatartacciyar ‘yar jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne kwanan nan a wajen ƙaddamar da shirin ba da tallafin kuɗi ga mabuƙata, a turance ‘Cash Grant for Vulnerable Groups’ wanda aka yi a zauren majalisa na Gidan Gwamnati a Gusau.

Gwamna Matawalle ya lissafa alfanun da jihar sa ta samu daga Shirye-Shiryen Inganta Rayuwar Jama’ar Ƙasa (NSIPs), sannan ya yaba wa Ministar da Shugaba Muhammadu Buhari saboda ƙoƙarin su na rage fatara da yunwa a Nijeriya.

Ya ce: “Ministar ta na ta ƙoƙarin tabbatar da cewa ita nagartacciyar ‘ya ce daga jihar mu. Hakan a bayyane ya ke idan an yi la’akari da jerin shirye-shiryen Gwamnatin Tarayya na agajin jama’a wanda ma’aikatar ta ke aiwatarwa, waɗanda jihar mu ta amfana ƙwarai da gaske daga gare su.

“Haka kuma mun ga haka ta wajen ƙaunar da ta ke nuna wa wannan gwamnatin a kowane lokaci.

Gwamna Matawalle da Minista Sadiya su na mika cakin kudi ga mata masu sana’a a lokacin taron

“Na fahimci cewa ministar ta zo Jihar Zamfara ne domin ta rarraba kayan abinci da sauran kayayyaki ga ‘yan gudun hijira, kuma ta ƙaddamar da Shirin Ba Da Tallafin Kuɗi ga Mabuƙata, kuma ta raba takardun kama aiki ga ma’aikata ‘yan sa ido masu zaman kan su da aka ɗauka, sannan kuma ta ba da rance maras ruwa ga manoma da mata ‘yan kasuwa. 

“Waɗannan abubuwan hoɓɓasa da ake yi wasu muhimman matakai ne da ake ɗauka domin a rage fatara tare da ƙarfafa wa mutanen mu gwiwa ta fuskar tattalin arziki. Halin ƙunci da ake ciki a ƙasar nan ya na buƙatar gwamnatoci a kowane mataki su dage su yi aiki wurjanjan. Wannan ƙoƙarin ya na zuwa ne a matsayin ɗori a kan ƙoƙarin da gwamnatin wannan jihar ke yi ta fuskoki da dama

domin ta sauƙaƙa wa jama’ar wannan jihar.”

A nata jawabin, Minista Sadiya Umar Farouq ta bayyana cewa ma’aikatar ta za ta raba agajin kuɗi ga mabuƙata 4,728 da ke Ƙananan Hukumomi 14 da ke faɗin jihar, yayin da an tantance tare da lissafa mutum 4,616 da za su ci moriyar lamunin Shirin Tallafin Kasuwanci na Gwamnati (wato GEEP) wanda babu ruwa a cikin sa, wanda ya kama daga N50,000 zuwa N300,000.

Ministar ta kuma ƙaddamar da Shirin Faɗakarwa na Ƙasa kan Shirin Ciyar Da Ɗalibai tare da ɗaukar ma’aikata ‘yan sa ido su 130, da sauran ayyuka.

A Jihar Zamfara dai, mutum 800 ne masu cin moriyar waɗanda su ka haɗa da naƙasassu da kuma tsofaffi waɗanda za a ba kyautar N50,000 kowannen su.

Hajiya Sadiya Umar Farouq ta na kaddamar da shirin ciyar da ‘yan makaranta a Gusau

Daga bisani, ministar ta ziyarci ɗaya daga cikin sansanonin ‘yan gudun hijira inda ta raba kayan abinci da sauran kayan masarufi, ta kuma ƙaddamar da wani laburare tare da raba kayan cin abinci ga ‘yan makaranta a ƙarƙashin Shirin Ciyar Da ‘Yan Makaranta.

Loading

Previous Post

Jarumin Kannywood Umar Yahaya Malumfashi (Bankaura) ya rasu

Next Post

Yadda aka yi jana’izar Umar Yahaya Malumfashi Bankaura

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Dandazon jama'a a wajen jana'izar Alhaji Umar Yahaya Malumfashi a maƙabartar Tarauni a Kano yau da safe

Yadda aka yi jana'izar Umar Yahaya Malumfashi Bankaura

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!