• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 16, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Shekara takwas na mulkin APC asara ce ga Nijeriya – Atiku

by DAGA WAKILIN MU
December 1, 2022
in Nijeriya
0
Atiku Abubakar ya na jawabi ga dandazon magoya bayan sa a taron PDP a Akure

Atiku Abubakar ya na jawabi ga dandazon magoya bayan sa a taron PDP a Akure

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ƊAN takarar zama shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya yi addu’ar kada Allah ya ƙara maimaita irin mulkin APC bayan 2023.

Atiku ya faɗi haka ne a lokacin da ya ƙaddamar yaƙin neman zaɓen sa na shiyyar Kudu-maso-yamma a Akure, babban birnin Jihar Ondo.

Da ya ke jawabi a wurin gangamin, wanda ya samu halartar ɗimbin magoya bayan PDP, Atiku ya ce Nijeriya ta yi asarar shekara takwas da APC ta yi ta na mulki, wanda su ka jefa jama’a cikin mawuyacin halin da ba shi misaltuwa.

Ya yi fatan cewa, “Daga 2023, kada Allah ya sake jarabtar ‘yan Nijeriya da irin mulkin APC.”

Wazirin na Adamawa ya yi alƙawarin farfaɗo da harkokin ilimi tare da inganta shi, ya na mai cewa, “Gwamnatin APC ta kashe harkar ilimi a ƙasar nan ta hanyar bijiro da tsare-tsaren da kowa ya san ba za su inganta cigaban ilmi ba.”

Ya ƙara jaddada irin alƙawarin da ya yi a Ilorin, wanda ya ce idan ya yi nasara, gwamnatin sa za ta ware dala biliyan 10 domin bunƙasa ƙanana da matsakaitan masana’antu, ta yadda matasa za su yunƙuro wajen samun aikin yi sosai, kuma su ma mata rayuwar su za ta ƙara bunƙasa.

Kafin ya fara jawabi, sai da uwargidan sa, Hajiya Titi Abubakar, ta fara yi wa dandazon magoya bayan PDP jawabi tukunna.

Titi, wadda haifaffiyar Jihar Ondo ce, ta ce ta yi farin cikin ganin PDP ta fara kamfen ɗin shiyyar Kudu-maso-yamma a jihar ta ta haihuwa.

Ta ce: “Ina gabatar da kai na a gare ku, a matsayi na na ‘yar ku. Idan ku ka zaɓi miji na, zai daƙile Boko Haram kuma zai inganta ilimi.

Dandazon mahalarta taron PDP a Akure

“Kada ku manta, miji na ne ya yi nasara a zaɓen 2019, amma aka yi masa maguɗi, aka murɗe zaɓen. To kada ku bari a sake yaudarar ku. Wannan lokacin ma ku fito ku sake zaɓen PDP.

“Idan Atiku ya yi nasara, wata dama ce da Jihar Ondo za ta samu cewa ‘yar su za ta zama uwargidan shugaban ƙasa. Da ma kuma Bayarabiya ba ta taɓa zama uwargidan shugaban ƙasa a Nijeriya ba.”

Da ta ke yabon mijin ta, Titi ta ce ko lokacin da ya na mataimakin shugaban ƙasa ya yi rawar gani, domin shi ne ya janyo irin su Nasir El-Rufai da Ngozi Okonjo-Iweala cikin gwamnati, “har da ma wasu fitattun haziƙan da su ka kawo cigaba a ƙasar nan.”

Mataimakin takarar Atiku, Gwamna Ifeanyi Okowa, shi ma ya ce PDP za ta farfaɗo da fannin ilimi. Sannan ya nuna damuwar sa dangane da yadda ɗaliban jami’a su ka shafe watan takwas a gida, ya na mai cewa ba za a samu irin haka a gwamnatin su ba.

Shi ma Gwamna Udom Emmanuel ya roƙi al’ummar Jihar Ondo da su zaɓi Atiku, wanda ya ce shi kaɗai a cikin sauran ‘yan takarar zai iya haɗa kan Nijeriya.

Shugaban jam’iyyar PDP, Iyorchia Ayu, da Babban Daraktan Kamfen, wato Gwamna Aminu Waziri Tambuwal na Sokoto, duk sun yi wa taron jawabai masu nuna fifikon Atiku kan sauran ‘yan takara.

Loading

Tags: AkureAminu Waziri TambuwalAtiku AbubakarIyorchia AyukamfenOndoTiti Abubakaryaƙin neman zaɓeZaɓen 2023
Previous Post

Hotuna: An karrama ‘yan Kannywood da sauran jama’a a bikin ‘Henna Ball’ karo na 7

Next Post

Batun A’isha Buhari: Ni ma ba zan iya ɗaukar wulaƙancin yaran soshiyal midiya marasa tarbiyya ba – Mansurah Isah

Related Posts

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista
Nijeriya

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista

June 13, 2025
Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus

June 4, 2025
Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150
Nijeriya

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150

May 31, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta goyi bayan amfani da Ƙirƙirarrar Basira cikin ɗa’a a aikin jarida – Idris
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a ambaliyar garin Mokwa

May 30, 2025
Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris
Nijeriya

Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris

May 25, 2025
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris
Nijeriya

Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris

May 20, 2025
Next Post
Mansurah Isah

Batun A'isha Buhari: Ni ma ba zan iya ɗaukar wulaƙancin yaran soshiyal midiya marasa tarbiyya ba - Mansurah Isah

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!