• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 16, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Shugaban INEC ya na so ma’aikatan hukumar su jajirce a zaɓen Ondo

by DAGA WAKILIN MU
October 9, 2020
in Nijeriya
0
Farfesa Mahmood Yakubu, Shugaban INEC

Farfesa Mahmood Yakubu, Shugaban INEC

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
SHUGABAN Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya yi kira ga ma’aikatan hukumar da su tabbatar da cewa sun ci gaba da aiki tuƙuru tare da tsare gaskiya don samun irin nasarar da su ka yi a Jihar Edo kwanan nan a zaɓen da za a yi ran Asabar ɗin nan a Jihar Ondo.
 
A saƙon da ya miƙa ga ma’aikatan hukumar ran Alhamis don ƙara masu ƙwarin gwiwa, shugaban ya ce, “Tilas ne mu jaddada nasarar da mu ka samu kwanan nan don tabbatar da cewa kowace ƙuri’a da aka kaɗa a ranar 10 ga Oktoba ta yi amfani wajen tabbatar da cewa wanda mutane su ka zaɓa shi ne ya ci zaɓen.
 
“Saboda haka ina kira a gare ku baki ɗaya da ku guji duk wani kwaɗayi, ku tabbatar dukkan abin da ku ka yi ya na kan doka da  kuma tsoron Allah.
 
“Ko yaushe ku tuna da cewa duk wani abu da wani ma’aikacin INEC ya aikata zai iya shafar dukkan mu.
 
“Ku kasance cikin shiri da riƙe gaskiya kuma ku sadaukar da kan ku ga manufofi da burin Hukumar.”
 
A saƙon nasa, shugaban na INEC ya ce: “Kamar mako uku da su ka gabata, ana gobe za a yi zaɓen Gwamnan Jihar Edo, na yi kira ga ma’aikatan Hukumar nan masu aiki tuƙuru da su maida hankali wajen ganin sun bi hanyar gaskiya, mai nagarta, kuma bisa tsarin da mu ke da shi. 
 
“Tabbas, ma’aikatan mu, tare da taimakon hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki, ba su yi ƙasa a gwiwa ba wajen tabbatar da nasara a wajen zaɓen. 
 
“A bayyane ya ke cewa ‘yan Nijeriya da abokan Nijeriya sun yi murna da sakamakon zaɓen, kuma mun samu ƙwarin gwiwa daga yabon da su ka yi mana.
 
“Duk da haka, kada mu kuskura mu yi sanyi a aikin mu. Ga wani zaɓen Gwamna ɗin ya zo mana. Yanzu an ma fi saka ido a kan Jihar Ondo. Tilas ne mu jaddada nasarar da mu ka samu kwanan nan don tabbatar da cewa kowace ƙuri’a da aka kaɗa a ranar 10 ga Oktoba ta yi amfani wajen tabbatar da cewa wanda mutane su ka zaɓa shi ne ya ci zaɓen.”
 
A ƙarshe, Farfesa Yakubu ya yi godiya a gare su saboda ƙoƙarin su.

Loading

Previous Post

Gasar Aminiya- Trust: An fidda gwarzaye 20 na matakin kusa da ƙarshe

Next Post

ZPreety: Babban buri na shi ne…

Related Posts

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista
Nijeriya

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista

June 13, 2025
Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus

June 4, 2025
Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150
Nijeriya

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150

May 31, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta goyi bayan amfani da Ƙirƙirarrar Basira cikin ɗa’a a aikin jarida – Idris
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a ambaliyar garin Mokwa

May 30, 2025
Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris
Nijeriya

Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris

May 25, 2025
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris
Nijeriya

Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris

May 20, 2025
Next Post
ZPreety: "Asali ba fim na ke son yi ba"

ZPreety: Babban buri na shi ne...

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!