SHUGABA Bola Ahmed Tinubu ya nuna matuƙar jimami kan rasuwar Alhaji Abbas Sanusi, Galadiman Kano kuma uba a masarautar Kano.
Mariganyin ya rasu yana da shekaru 92 bayan jinya mai tsawo.
Ya bar ’ya’ya da jikoki da dama.
Ɗaya daga cikin ’ya’yan sa shi ne Alhaji Abdullahi Abbas, Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano.
Tinubu ya bayyana mariganyin a matsayin ginshiƙi mai ƙarfi na masarautar Kano, wanda ya bayar da gudunmawa sosai wajen cigaban ta da ɗorewar ta.
Shugaban ya jaddada cewa irin ayyukan alheri da marigayin ya yi tun daga shekarar 1959, lokacin da ya karɓi sarauta, za su kasance abin alfahari ba kawai a masarautar Kano ba, har da Jihar Kano baki ɗaya da ma ƙasa gaba ɗaya.
Shugaban ya yi ta’aziyya ga gwamnatin jihar da masarautar Kano da iyalan mamacin bisa wannan babban rashi.
Daga ƙarshe, Shugaban ƙasa ya roƙi Allah ya gafarta wa mariganyin, ya sanya shi cikin Aljannar Firdausi, tare da ba iyalan sa haƙurin jure rashin da suka yi.
![]()






