GWAMNATIN Tarayya ta bayyana cewa za ta fara biyan ma’aikata da sabon tsarin ƙarin albashi daga ranar 1 ga Afrilu, 2024.
Ministan Yaɗa da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana haka a ranar Alhamis, a Abuja, lokacin da ya ke tattaunawa da manema labarai.
Idris ya ce gwamnati za ta daina biyan N30,000 a matsayin mafi ƙanƙantar albashi daga ƙarshen watan Mayu, 2024.
Bayan wani nazari mai zurfi da majiɓinta kula da harkokin kuɗaɗen Gwamnatin Tarayya su ka yi, an bayyana cewa gwamnatin za ta kashe naira tiriliyan 24.66 a shekarun 2024, 2025 da 2026 wajen biyan albashi.
Bayan Shugaba Bola Tinubu ya cire tallafin fetur a ranar 29 ga Mayu, 2023, sai Gwamnatin Tarayya ta bijiro da ƙarin N35,000 kan gundarin albashin kowane ma’aikacin a matsayin tallafin rage raɗaɗin tsadar rayuwa na wani taƙaitaccen lokacin watanni shida.
To sai dai kuma a lokacin, Kungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC) ta tayar da ƙayar baya cewa tallafin na toliyar N35,000 kan albashin ma’aikata, lasa zuma a baki ne, tunda ba na dindindin ba ne.
Maimakon haka, ‘yan ƙwadago sun karci ƙasa tare da jajircewa lallai sai dai a yi ƙarin albashi ɗungurungum a 2024.
Bayan shafe watanni ana je-ka-ka-dawon tattaunawa, wakilan Gwamnatin Tarayya ta da na Majalisar Tarayya da Al’amurran Ma’aikatan Tarayya (NPCNC), sun cimma amincewa dangane da batun N30,000 mafi ƙanƙantar albashi daga ranar 18 ga Oktoba, 2019.
Sai dai kuma a ranar Alhamis ƙungiyoyin ƙwadago sun bayyana cewa sun fara tattaunawa da Gwamnatin Tarayya, tare da jaddada cewa dokar biyan haƙƙin leburan Gwamnatin Tarayya ta shar’anta cewa duk bayan shekaru biyar a riƙa yi wa ma’aikata ƙarin albashi.
![]()






