1. Allah ya na ɗaukaka duk wanda ya so, malami ko jahili, yaro ko babba, mace ko namiji.
2. Sannan alƙawarin Allah ne cewa komai ya ɗaga sama zai sauko ban da zatin Ubangiji.
3. Wasu su kan yi ‘safe landing’, wasu kuma ‘crash landing’.
4. San da aka ɗaukaka ka, ba a yi shawara da kai ba, san da za a sauko da kai ma ba za a yi shawara da kai ba.
5. Me ya sa sai bawa ya riƙa haɗawa da tsafe-tsafe, ƙulumboto da tsibbace-tsibbace wai don ɗaukakar sa ta ɗore? To, a irin haka ne idan Allah ya nuna maka Shi ne mai yi sai ka ga mutum ya shiga damuwa sakamakon faɗowa ƙasa da ya yi har ta kai ga ya na neman faɗawa damuwar da za ta sa ya shiga halin ƙaƙa-na-ka-yi.

LADUBBAN SHAHARA
Idan Allah ya ɗaukaka ka ka zamo:
1) Mai bin Allah in Musulmi ne kai, ko da ko Musulmi ko ba Musulmi ba, ka zamo mai kunya a cikin shaharar ka daidai yadda al’adar ka ta ke.
2) Ka riƙe iyaye, ‘yan’uwa da abokai da su ka san ka tun kafin ka zama.
3) Ka kyautata mu’amalar ka da masoyan ka masu bin ka don Allah da masu bin ka saboda ɗaukakar ka.
4) Ka yi taka-tsantsan da waɗanda ke zagaye da kai su na ce maka kai kaɗai ne, wai babu kamar ka.
5) Yi ƙoƙari ka gina rayuwar gobe, ka yi tattali kafin ɗaukakar ta kuɓuce maka.
6) In ba ka da ilimi, ka nema ko wane iri ne, zai taimaka maka.
7) Ka ɗauki shawarwarin da mutanen nesa da kai su ke ba ka; ba kowane na kusa da kai ne zai ba ka shawara ka ɗauka ba sai daidai, ma’ana waɗanda ka yaba da hankalin su.
8) Yi ƙoƙari ka gane masoya da maƙiya cikin hikima, kowa ka san yadda za ka zauna da shi.
9) Ka cire kwaɗayi, ka ƙara haƙuri, ka ji tsoron Allah, sai ka tsira daga ashararan mutane masu bin ɗaukaka don biyan buƙata.
10) Ka riƙe iyayen ka da kyau in su na raye, in ba sa raye ka kyautata wa abokan su da waliyan ka, shin ‘yan’uwa ne ko kuma maƙota.
HAZA HUWA MA INDEE WA BILLAHIT TAUFEEQ.
Malam Mudassir Ƙasim fitaccen sha’iri ne mazaunin birnin Kano