TSOHUWAR jarumar Kannywood, Hajiya Zakiyya Ibrahim Abdullahi, ta bi sahun wasu jarumai mata ta yi auren ba-zata.
An ɗaura mata aure da sahibin ta, Abubakar Mika’il, da misalin ƙarfe 1 na ranar Juma’a da ta gabata, 12 ga Yuli, 2024 a Masallacin Juma’a da ke unguwar Chiranchi a cikin birnin Kano.
Sai dai jama’a da dama ba su san da wannan auren ba har sai bayan an ɗaura.

Amarya Zakiyya ta tabbatar wa da mujallar Fim cewa an ɗaura mata aure, inda ta ce, “Gaskiya ne an ɗaura aure na ranar Juma’ar da ta gabata, Kuma ina shirin tarewa a ranar Asabar idan Allah ya kai mu.
“Alhamdu lillahi, ina godiya da Allah ya nuna mini wannan rana. Kuma ina fatan Allah ya ba mu zaman lafiya ni da miji na, ya kawar da dukkan fitina a tsakanin mu.”
To, mu ma mun ce amin.
Jaruman Kannywood mata da su ka yi irin wannan auren na ba-zata a cikin ‘yan watannin nan sun haɗa da Hajiya Rashida Adamu Abdullahi Maisa’a (a cikin 2023), sai Hajiya Fati KK, Hajiya Mansurah Isah da kuma Hajiya Sadiya Gyale (a cikin 2024).