JARUMAR Kannywood, Hajiya Asma’u Sani, ta bayyana cewa ‘yan’uwan ta ‘yan fim da kuma marubuta littattafai sun fitar da ita kunya da irin karar da suka yi mata a bikin auren ‘yar ta, A’isha Ibrahim Yusuf, wanda aka kammala.
Asma’u ta bayyana hakan ne a hirar da ta yi da mujallar Fim a lokacin da take bayyana ɗimbin farin ciki tare da godiya ga mahalartan bikin.
Ta ce: “To alhamdu lillah, duk da ka same ni a cikin baƙi ana kusa da kammala taron bikin auren ‘ya ta kuma autar mata a cikin ‘ya’ya na, da man matan biyu ne, Sumayya Abubakar, matar Jamilu Ibrahim, sai kuma wannan A’isha, ita ma ga shi Allah ya nuna mana lokacin auren ta. Kuma alhamdu lillah, ina ƙara godiya ga Allah.

“Ina yin hidimar taruka iri-iri tun daga auren Sumayya da kuma sunan ‘ya’yan da ta haifa duk taron bukukuwa ana yi, amma ban taɓa yin hidima irin wannan ba. Gaskiya ban taɓa tara mutane irin wannan ba.
“Alhamdu lillah, ko a na Sumayya da Jamilu an taru, sai dai a yanzu da yake an ƙara samun arzikin ɗaukaka, jama’a sun ƙaru, don haka mutane daga garuruwa daban-daban, baƙi babu inda ba a zo ba. Legas, Nassarawa, Kaduna Abuja, Gombe duk da sauran garuruwa sun zo wajen wannan taron bikin.
“Kuma alhamdu lillah, gaskiya na ga taro na ga soyayya a wajen mutane. Babu abin da zan ce, sai dai na ce na gode wa Allah.
“Kuma a gaskiya jarumai na masana’antar finafinai ta Kannywood sun yi mini kara sun ba ni mamaki, ‘yan’uwa na jarumai sun fitar da ni kunya.
“Na sani ni ta mutane ce, kuma ina zaune da mutane lafiya, ba na rigima da kowa, kowa ya san ni da haka. Amma yadda jarumai suka yi mini kara wallahi na yi mamaki. Sun yi kara sun zo wajen biki an yi hidima sosai an yi abubuwa. Sun yi alheri a wajen taron bikin, sun fitar da ni kunya.

“Haka nan marubuta su ma sun zo don ina cikin su, dukkan su ƙawaye na ne. Don Bilkisu Yusuf Ali aminiya ta ce sosai, babu inda ba na shiga a cikin gidan su, haka ita ma take a gidan mu. To duk sun zo sun yi mini kara.
“Irin su Fauziyya D. Sulaiman, Hadiza Nuhu Gudaji, Bushira Nakura, Sadiya Garba Yakasai, Lubabatu Ya’u, duk da sauran su, marubuta dai su ma sun yi mini kara.
“Ga kuma oga na, Ado Ahmad Gidan Dabino MON, kuma shugaban mu na MOPPAN kuma sarki na mawallafa.”
Uwar amaryar ta ce akwai darasin da ta koya daga wannan taro.
“Gaskiya alhamdu lillah, wannan taro na samu darasi sosai, domin babban darasin da na samu a tara jama’a shi ne kana so ka sallami waɗancan, kuma ga wasu sun zo, wani ma gani yake yi kamar ka ƙi kulawa da shi. Kuma ba haka ba ne. Kowa so kake ka ba shi haƙƙin sa a matsayin sa na baƙon ka, masoyin ka.
“To alhamdu lillah na sake samun ƙaruwa ta ilimi a kan wannan.”
Ta ƙara da cewa: “Duk abubuwa ga su nan sun gudana, don haka sai an yi haƙuri idan aka tara jama’a.
“Kuma ina godiya ga Allah da kuma ɗimbin jama’ar da suka halarci taron bikin. Wanda aka saɓa wa, ya yi haƙuri, ba da sani ba aka yi hakan ba. Kowa nawa ne saboda yana so na ya zo don haka ba zan yi abin da zai ɓata masa ba ina sani.
“Allah ya kai kowa gidan sa lafiya.”
Asma’u ta ba da shawara ga amarya da kuma surukin ta, ta ce, “Amarya da ango su yi haƙuri, Allah ya ba su haƙuri na zama da juna, domin kuwa shi zaman aure zama ne na zo mu zauna zo mu saɓa, tunda ana zama tare wani zai saɓa wa wani. Shi zai iya yi mata laifi, ita ma za ta iya yi masa. Don haka sai an yi haƙuri da juna a rinƙa yin sulhu a tsakani ba sai an tafi wani waje ba.
“Allah ya kawar da fitina a tsakanin su, ya ba su zaman lafiya. Ina godiya sosai. Allah ya saka wa kowa da alheri.”