SHUGABAN riƙo na jam’iyyar APC na Ƙasa kuma tsohon Gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, tare da Ministar Fasaha, Raya Al’adu da Harkokin Nishaɗantarwa, Hajiya Hannatu Musawa, sun karɓi baƙuncin ‘yan masana’antar shirya finafinan Hausa da ke cikin jam’iyyar, a ƙarƙashin ƙungiyar su ta ‘Kannywood APC Stakeholders Forum’.
Mujallar Fim ta samu labarin cewa a zaman da su ka yi a hedikwatar APC ta ƙasa a yau, sun tattauna kan hanyoyin da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu za ta iya inganta harkar masana’antar finafinai ta Kannywood.

‘Yan Kannywood ɗin sun haɗa da manyan furodusoshi da mawaƙa da jarumai irin su Sani Mu’azu, Aminu Hudu (Almah), Ali Nuhu, Falalu Ɗorayi, Mansurah Isah, Muddassir Ƙasim, Asma’u Sani, Fati Nijar, Jamila Nagudu, Abdul Amart, Umma Shehu, da Hadiza Kabara.
Sun kai ziyarar a ƙarƙashin jagorancin Malam Khalid Musa.



