• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, July 1, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Zaɓen 2023: Ko Kanawa za su zaɓi ‘yan fim?

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
September 30, 2022
in Nijeriya
0
Fastocin yaƙin neman zaɓe na wasu 'yan Kannywood: Abale, Ala, Awilo da Daddy

Fastocin yaƙin neman zaɓe na wasu 'yan Kannywood: Abale, Ala, Awilo da Daddy

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

A DAIDAI lokacin da ake musayar ra’ayi kan buga kugen fara yaƙin neman zaɓe na shekarar 2023 wanda Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta yi a jiya, mujallar Fim ta hango cewa akwai ‘yan fim na masana’antar finafinai ta Kannywood waɗanda tuni su ke cikin harkokin zaɓen dumu-dumu. A baya ‘yan Kannywood da ke Kano sun sha shiga siyasa ana damawa da su, amma dai sau da yawa a matsayin masu tallar ɗan takara da kuma jam’iyyar siyasa aka san su, sai ƙalilan da su ka fito takara, wato irin su Hamisu Lamiɗo Iyan-Tama da ya taɓa yin takarar zama gwamna. A jihar ta Kano, babu wani ɗan fim da ya taɓa tsallake ko da zaɓen fidda gwani a jam’iyyar da ya fito.

To, a wannan karon dai an samu canji, ‘yan fim sun ci gaba a fagen siyasa a Kano. Mujallar Fim ta gano cewa akwai waɗanda su ka fito takara har su ka tsallake siraɗin zaɓen fidda gwani, jam’iyya ta tsai da su a matsayin gwanayen ta a babban zaɓen na 2023.

A Ƙaramar Hukumar Nassarawa, mawaƙi Aminu Ladan Abubakar Ala ya na takarar Majalisar Wakilai a jam’iyyar ADP. A Ƙaramar Hukumar Gwale, tsohon furodusa Abdulhadi Ɗalhatu (Awilo) ya na takarar zuwa Majalisar Dokoki ta Jihar Kano a jam’iyyar PDP. Ali Rabi’u Ali (Daddy) ya na takarar Majalisar Wakilai mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Dala a jam’iyyar PRP.

Shi kuwa jarumi Adamu Abdullahi Adamu (Daddy Hikima), wanda aka fi sani da Abale a cikin shirin ‘A Duniya,’ ya samu tsayawa takarar Majalisar Wakilai mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Kumbotso a jam’iyyar ADP.

Irin wannan fitowa takara ta ba-zata da ‘yan fim su ka yi a Jihar Kano, har su ka yi nasarar lashe zaɓen cikin gida a jam’iyyun su, ya ba su damar mutanen jihar su zaɓe su, musamman ma yanzu da ake faɗin “mutum za a zaɓa, ba jam’iyya ba.”

A yanzu babu wanda zai iya yanke hukuncin cewa ‘yan fim ɗin nan da ke takara za su kai gaci a zaɓen ba baɗi ko a’a; Allah kaɗai ya sani. Lokaci da yanayi ne kaɗai za su bayar da amsa.

Loading

Previous Post

Masu zargin ina saka kalmomin batsa a cikin waƙoƙi na su daina – Kawu Ɗan Sarki

Next Post

Wace cuta ke damun Fati Bararoji?

Related Posts

Tawagar Gwamnatin Tarayya ta miƙa saƙon ta’aziyya daga Tinubu tare da yin addu’o’i a gidan Ɗantata a Madina
Nijeriya

Tawagar Gwamnatin Tarayya ta miƙa saƙon ta’aziyya daga Tinubu tare da yin addu’o’i a gidan Ɗantata a Madina

June 30, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta bada tabbacin akwai tsaro a Abuja duk da gargaɗin da Amurka ta ba matafiya

June 23, 2025
Kiran Gwamnatin Tarayya ga ‘yan jarida: Ku zama jigo wajen gina dimokiraɗiyyar Nijeriya
Nijeriya

Kiran Gwamnatin Tarayya ga ‘yan jarida: Ku zama jigo wajen gina dimokiraɗiyyar Nijeriya

June 21, 2025
Ministan Yaɗa Labarai ya yaba wa Hafsoshin Soji kan cigaban da aka samu a fannin tsaron ƙasa a shekaru biyu
Nijeriya

Ministan Yaɗa Labarai ya yaba wa Hafsoshin Soji kan cigaban da aka samu a fannin tsaron ƙasa a shekaru biyu

June 20, 2025
Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista
Nijeriya

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista

June 13, 2025
Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus

June 4, 2025
Next Post
Fati Baffa ta ce ta yi mamakin masu surutu game da ita

Wace cuta ke damun Fati Bararoji?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!