A YAU Juma’a za a ɗaura auren tsohuwar jarumar Kannywood, Sadiya Muhammad Tukur, wadda aka fi sani da Sadiya Gyale.
Za a ɗaura auren Safiya da sahibin ta, Mustapha Umar, a masallacin Juma’a na Phase 3 da ke unguwar Sharaɗa a cikin garin Kano da misalin ƙarfe 2.
Kamar yadda katin gayyatar ɗaurin auren da Sadiyar ta turo wa mujallar Fim ya nuna, za a ɗaura auren ne bayan sallar Juma’a.
Sai dai kamar yadda ta shaida mana za a yi taron ɗaurin auren ne kawai, amma babu wasu shagulgulan biki da za a yi kamar yadda ‘yan fim suka saba yi.
Wannan shi ne auren Sadiya Gyale na biyu. Ta taɓa auren wani mutum mazaunin Kaduna shekaru tara da suka gabata, amma auren ya mutu kafin ta tare. Daga baya Allah ya yi masa rasuwa.
Allah ya ba su zaman lafiya da ƙaruwar arziki, amin.

