WATA kotu a birnin Kano a yau ta yanke wa jaruma kuma furodusar finafinan Hausa, Sayyada Sadiya Haruna, hukuncin komawa Islamiyya.
Sadiya dai ta shahara wajen sayar da kayan ƙarin ni’ima da na ƙarfin maza ta hanyar soshiyal midiya, kuma tsarin yin tallar ta ya na ba wasu mutanen mamaki ko haushi, wanda hakan ne ya sa jami’an Hukumar Hisba su ka kama ta a ranar Juma’a da ta gabata, 20 ga Agusta, 2021.
Hukumar ta damƙa ta ga hannun rundunar ‘yan sanda ta Jihar ta Kano, su kuma ‘yan sandan su ka maka ta a kotun shari’ar Musulunci da ke Hukumar Hisbah ta Jihar Kano bisa zargin yaɗa hotunan batsa a kafafen sada zumunta da sunan sana’a.
‘Yan sandan sun gurfanar da kyakkyawar jarumar ne a gaban Mai Shari’a Ali Jibril Ɗanzaki, wanda shi kuma bayan an gabatar masa da bayanai sai ya yanke mata hukuncin sanya ta a makarantar Islamiyya mai suna Darul Hadith har na tsawon wata bakwai.
Ɗaya daga sharuɗɗan da alƙalin ya gindaya mata shi ne za ta riƙa zuwa makarantar tare da rakiyar jami’an Hukumar Hisba.
Haka kuma ya bayyana cewa a duk sa’ilin da ta je makarantar, za ta riƙa sa hannu a wata takarda, shaidar ta je ɗin.
Daga nan aka sake ta, ta tafi gida.
Wakilin mujallar Fim ya so jin ta bakin jarumar kan wannan hukunci da aka yanke mata, amma abin ya faskara.

Ita dai Sayyada Sadiya Haruna, da yawa su na mata kallon ‘yar taratsi, wadda ke amfani da kalaman batsa da rawar kai a bidiyoyin tallar kayan gyaran jiki da na ƙarin ni’ima da ƙarfin maza. Haka kuma ta kan yawan ambaton ƙirar jikin ta da kyan fuskar ta.
To amma kuma ta kan shirya bidiyoyin waƙoƙin yabon Manzo Allah (s.a.w.), inda ake nuno ta ta na bin waƙoƙin bege da wasu su ka rera.
Ta raɗa wa kan ta laƙabin Sayyada domin nuna shauƙin ta game da son Manzon Allah (s.a.w.).
Kama ta da ‘yan Hisba su ka yi ya jawo ka-ce-na ce a soshiyal midiya, inda wasu ke cewa an kyauta, ya kamata a ɗaure ta, to amma wasu kuma na cewa sam ba daidai ba ne.
Jaruma Ummah Shehu na daga cikin masu kare Sadiya, ta na faɗin cewa kama ta da aka yi an keta mata mutunci kuma Allah ya ce ba a shiga tsakanin sa da bawan sa.
Wasu masu maganar sun yi wa Umma Shehu caa, su na cewa sam ba ta nuna kishin Musulunci ba kuma kama Sadiya abu ne da ya dace.