BAYAN gaisuwa mai yawa tare da fatan ka na lafiya. Allah sanya haka, amin.
Bayan haka, ba tare da ɓata lokaci ba, na rubuto maka wannan saƙo ne da nufin jin inda aka kwana dangane da babban abin alherin da ka yi iƙirarin ka aikata a bara (Oktoba 2020), inda ka sanar da al’umma cewa ka fidda zunzurutun kuɗi, kimanin naira miliyan 47, domin ɗaukar nauyin karatun wasu yara marayu sama da 100, a wata makaranta mai zaman kan ta, mai suna ‘Professor Ango Abdullahi College’.
Babban dalilin da ya sanya na tado maka da wannan batu shi ne, saboda a bara, daidai lokacin nan, al’amarin naka ya tada ƙura a nan kafafen sada zumunta na soshiyal midiya da kuma jaridu, mujallu, rediyo da talabijin.
A wancan lokacin, mutane da yawa sun riƙa tababa da kokwanto kan al’amarin, har ma wasu kai-tsaye su ka ƙaryata ka, wasu ma har su ka nemi taɓa mutuncin ka.
Idan ba ka mance ba, ni kai na daga jaridar Aminiya na kira ka a waya sau uku, ba ka ɗaga ba, kuma na turo maka tes amma ka ƙi amsa tambayar mu. Haka mu ka gaji mu ka buga labarin ta hanyar abin da mu ka samu daga hukumar makarantar da kuma wani ɓangare na fadar Mai Martaba Sarkin Zazzau.
Haka kuma, a barar dai, manyan ‘yan jarida na Arewa, kamar Malam Ibrahim Sheme da Malam Jaafar Jaafar, duk sun yi ƙoƙarin bin diddigin al’amarin ba tare da samun gamsasshen bayani ba.
A yanzu, na tado da bayanin nan ne domin mu ji daga bakin ka, shin me ake ciki game da wannan babban aikin alheri da ka ce ka ɗabbaƙa a bara? Har yanzu ka na ci gaba da ɗaukar nauyin yaran nan kuma wane matakin karatu su ke a yanzu?
Amsoshin da ka bayar za su inganta al’amarin nan kuma ka wanke wa masu kokwanto dukkan shakku. Haka kuma aikin naka zai zama abin koyi daga jaruman fim irin ka, kasancewar duk wanda ya assasa alheri kuma aka yi koyi da shi, zai rabauta ninkin-ba-ninkin.
Wassalam. Ina yi maka fatan alheri!
* Malam Bashir Yahuza Malumfashi shi ne Editan Labarai na jaridar Aminiya
![]()







