FITACCEN mawaƙi Alhaji Dauda Abdullahi Kahutu (Rarara) ya auri daɗaɗɗiyar aminiyar sa, Hajiya Aisha Ahmad Idris (A’ishatulhumaira) a yau a Maiduguri, Jihar Borno.
An ɗaura auren a kan sadaki N500,000 bayan sallar Juma’a, kuma an biya lakadan.
Ɗimbin jigajigan ‘yan siyasa sun halarci ɗaurin auren. Sun haɗa da tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Aminu Bello Masari, da Mataimakin Kakakin Majalisar Dattijai, Sanata Barau Jibril.
Mai taimaka wa Shugaban Ƙasa na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Malam Abdulaziz Abdulaziz, shi ya jagoranci tawagar shugaban ƙasa zuwa wajen ɗaurin auren.
A ‘yan fim kuma akwai manyan aminan angon, wato Alhaji Isma’il Na’abba Afakallahu da Malam Baban Chinedu.

Ɗaurin auren ya ba mutane mamaki duk da yake kusan kowa ya san danyen ganyen da ke tsakanin aminan biyu.
A tsawon shekaru, ko wa ya ga zara, to zai ga wata, wato duk inda aka ga mawaƙin, to za a gan shi tare da Aisha wadda ita ce manajar kuɗin da kuma ‘yar amshi a duk dandalin da ya bayyana domin waƙa.
Amarya A’ishatulhumaira dai furodusa ce kuma jaruma a Kannywood, kuma tana taɓa harkar kasuwanci.
A yanzu ta zama mata ta huɗu ta Rarara, wanda yana da mata uku kafin wannan auren.
Ɗaurin auren ya burge mutane matuƙa.
Kowa yana yi masu fatan alheri tare da addu’ar Allah ya ba su zaman lafiya.

