KWANAN nan ne jarumi a Kannywood, Malam Adam M. Adam, ya shirya wata ‘yar liyafa ta musamman a gidan sa shi da iyalin sa domin murnar cika shekaru 10 da auren su shi da matar sa, Hajara. An ɗaura auren su a cikin Agusta 2015, wanda ya nuna a yanzu sun cika shekaru 10 cur a matsayin ma’aurata.
Wannan ba ƙaramar nasara a aure, musamman a wannan zamanin da wani auren ma ko shekara ɗaya ba ya yi.
Saboda farin ciki, jarumin ya yi wa mujallar Fim ƙarin bayani game da shekaru 10 da auren nasu, kamar haka:
“Alhamdu lillah ina godiya ga Allah da ya nuna mana lokacin da muka cika shekaru goma da aure tsakani na da mata ta, Mrs. Hajara M. Adam, domin a yanzu mun cika shekara goma da zama ma’aurata.
“Mun yi aure a shekara ta 2015, kuma muna cikin soyayya da ƙaunar juna, da jin tausayin juna, da kuma daraja juna. Sannan mun samu ƙaruwar ‘ya’ya uku duk mata: Rumaisa M. Adam, Hauwa’u Hibba M. Adam da Fatima Sajida M. Adam.

“Wannan shekara goma da muka yi tun da na auri mata ta na kawo ta Kano daga Maiduguri, kullum iyayen ta da ‘yan’uwan ta sa mini albarka suke, haka ni ma iyaye na sa mata albarka suke yi, saboda tun da muka yi aure babu wanda ya taɓa jin kan mu da ita, kuma ba mu taɓa samun matsala da ita ba, wadda har sai wani ya ji.

“Ko da mun ɗan samu matsala ma, mu muke sasanta kan mu. Don haka babu abin da za mu ce da Allah sai dai godiya. Kuma muna cikin farin ciki da mu da ‘ya’yan mu.
“Muna roƙon Ubangiji Allah ya ƙara ba mu zaman lafiya da kwanciyar hankali a ƙasar mu da garin mu alfarmar shugaba S.A.W.”

![]()







