• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, July 1, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ƙungiyar furodusoshin Arewa ta kai wa sabon shugaban hukumar tace finafinai ziyara

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
August 2, 2023
in Labarai
0
Membobin Ƙungiyar Furodusoshi ta Arewa tare da Shugaban Hukumar Tace Finafinai Abba El-Mustapha

Membobin Ƙungiyar Furodusoshi ta Arewa tare da Shugaban Hukumar Tace Finafinai Abba El-Mustapha

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ƘUNGIYAR Furodusoshin Arewa (AFPAN), reshen Jihar Kano, ta ziyarci Babban Sakataren Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano, Alhaji Abba El-Mustapha, domin taya shi murnar sabon matsayin da ya samu.

Membobin ƙungiyar sun kai ziyarar ne a ranar litinin 31 ga Yuli, 2023 a ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙungiyar, Malam Gambo Musa, da mataimakiyar sa, Hajiya Mansurah Isah.

Da ya ke jawabi kan manufar ziyarar tasu, Gambo Musa ya ce sun je ne domin taya El-Mustapha murnar kama aiki da kuma fatan alheri.

Ya ƙara da cewa kasancewar El-Mustapha mutum mai kishin masana’antar Kannywood, sun san zai kai ta ga cigaban da ake buƙata fiye da yadda ake zato, don haka ne ma tun daga yanzu su ka yi wani tsari na karrama shi su ka so da hoton sa na musamman domin karrama shi.

Ya ce: “Don haka mu na yi maka fatan alheri da kuma samun nasara a jagorancin ka.”

Shugabannin ‘Arewa Film Producers Association of Nigeria’ (AFPAN) su na miƙa hoton musamman ga El-Mustapha

A nasa jawabin, El-Mustapha ya nuna farin cikin sa tare da godiya bisa zaɓar sa da ƙungiyar ta yi domin ta karrama shi, sannan ya yi wa ƙungiyar alƙawarin yin aiki tare domin kawo wa hukumar da kuma Jihar Kano cigaban da ake buƙata.

Shi dai El-Mustapha, tun bayan kama aikin sa a ranar 25 ga Yuli ɗaiɗaikun mutane da kuma ƙungiyoyi a Kannywood su ke yin tururuwa zuwa ofishin sa domin kai masa ziyara da kuma murnar kama aiki a matsayin sa na ɗan cikin su.

Rukunin farko da su ka fara kai masa ziyara su ne Majalisar Dattawan  Kannywood a ƙarƙashin jagorancin Malam Khalid Musa da su ka haɗu dukkan su su ka halarci ofishin don taya shi murna da yi masa fatan Allah ya taya shi riko.

Ita ma ƙungiyar ‘Kannywood Movement for Kwankwasiyya’ ta su furodusa Alhaji Sheshe ta kai irin wannan ziyarar ga El-Mustapha.

Ƙungiyar masu ba da umarni, wato ‘Screen Guild of Directors’ wadda Aminu S. Bono ya ke jagoranta, ita ma ta kai wa shugaban ziyarar taya murna da kuma fatan Allah ya sa ya yi jagoranci cikin adalci da sanin ya-kamata.

Haka ‘ya’yan ƙungiyar masu gala da ta ‘yan kasuwar fim su ma sun kai makamanciyar irin wannan ziyarar taya murna.

Shugaba Gambo Musa da mataimakiyar sa Mansurah Isah a lokacin miƙa hoton ga El-Mustapha
Shugabannin ‘Arewa Film Producers Association of Nigeria’ (AFPAN) a Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano

Loading

Previous Post

Marubutan Katsina sun yi sababbin shugabanni

Next Post

Soke lasisin ‘yan Kannywood: Hukumar Tace Finafinai ta canza shawara, za ta yi wa ‘yan fim rajista ta hanyar ƙungiyoyin su

Related Posts

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

June 22, 2025
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau
Labarai

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

June 22, 2025
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

June 22, 2025
Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano
Labarai

Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano

June 20, 2025
Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza
Labarai

Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza

June 20, 2025
Next Post
Sarari (na 2 daga hagu, a gaba) da El-Mustapha (da shuɗiyar riga)) sauran jami'ai a lokacin ziyarar

Soke lasisin 'yan Kannywood: Hukumar Tace Finafinai ta canza shawara, za ta yi wa 'yan fim rajista ta hanyar ƙungiyoyin su

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!