ƊIYAR fitaccen mawaƙin nan da ya riga mu gidan gaskiya, Alhaji Isyaku Muhammad Forest, za ta yi aure a ranar Lahadi, 11 ga Satumba, 2022.
Za a ɗaura auren A’isha Muhammad Forest da sahibin ta, Habibu Gambo Shu’aibu, da ƙarfe 11:00 na safe a masallacin Juma’a na Al-Ansar da ke unguwar Maidile, a Kano, kusa da gidan mahaifin ta.
Aminin marigayin, furodusa Usman Mu’azu, shi ne ya ba da sanarwar gayyatar ɗaurin auren a Instagram.
Idan masu karatun mu ba su manta ba, mujallar Fim ta ba da labarin rasuwar Isyaku Forest a ranar Asabar, 4 ga Satumba, 2021 a wani asibitin kuɗi da ke Titin Karkasara a Kano, bayan sha jinya.
Allah ya jiƙan sa, su kuma su A’isha da Habibu mu na addu’ar Allah ya ba su zaman lafiya da albarkar aure.
![]()







