JARUMIN barkwanci Mustapha Badamasi (Nabraska) ya bayyana cewa muƙamin da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na Jihar Kano ya ba shi na mataimaki na musamman a kan harkar farfaganda muhimmin aiki ne a gwamnatance, ba kamar yadda wasu ke kallon abin ba.
Tun bayan lokacin da gwamnan ya naɗa shi wannan matsayi dai wasu jama’a su ke ta tambaya kan ainihin manufar matsayin da aka baya shi. Wasu ma su na ganin kamar an mayar da shi wani shashasha ko wawan sarki ne fagen siyasa.
Sai dai a tattaunawar da mujallar Fim ta yi da shi, jarumin kuma ɗan siyasa ya fayyace yadda aikin nasa ya ke.
Ya ce: “Ita wannan kalmar mutane sun san ta amma sai ya zama kamar ba su fahimce ta ba, domin ita kalmar ‘farfaganda’ ko ‘kwarmato’ ana nufin isar da saƙo ne ga jama’a. Don haka ni an ɗana ni a matsayin mataimaki na musamman a gwamnatin Jihar Kano domin yaɗa abubuwan da gwamnati ta ke so ta isar ga jama’a.

Saboda haka aiki na wayar da kan jama’a a kan manufofin gwamnati da kuma wayar da kan jama’a a kan ayyukan ta da kuma kare muradun ta don kusanto da jama’a ga gwamnati.”
Da mu ka tambaye shi ko menene ya bambanta shi da waɗanda ake kira ‘yan midiya kuwa, cewa ya yi, “To ai su ‘yan midiya wasu za ka same su a cikin gwamnati, amma ba su da ofis; wasu kuma da yawa ba sa cikin gwamnati, kawai dai su na yi a matsayin ‘yan sa kai, sai kuɗin ‘data’ da ake ba su.
“Amma ni ka ga a matsayin ma’aikaci ne wanda na ke da ofis. Don haka ni fa ma’aikata kawai da ba ni da ita wadda ta ke ƙarƙashi na, amma ina da ofis kamar sauran ma’aikatan gwamnati.
“Don haka ina da shafi na da na buɗe na S.A. Farfaganda a YouTube da sauran kafafen sada zumunta don tallata manufofin gwamnatin Jihar Kano a matsayi na na S.A. Kwarmato.”
A matsayin sa na ɗan fim, ko wanne alfanu masana’antar Kannywood za ta samu ta ofishin sa? Sai Nabraska ya amsa da cewa: “Ai kuwa ta na samu, domin idan ka kula abubuwa da dama wannan gwamnati ta Abdullahi Umar Ganduje ta yi mana mu ‘yan fim ta hanyar ofishi na, kamar ɗaukar nauyin zaɓen shugabannin ƙungiyar MOPPAN na ƙasa, samar da gurbin karatu ga ‘yan fim a ƙasar waje, ga kuma na kwanan nan da aka yi taron horas da ‘yan fim na tsawon kwanaki biyar wanda tuni an gama kowa ya karɓi shaidar sa.

“To, ka ga wannan ai duk daga ofishi na aka same shi. Kuma mu na nan mun ci gaba da samar da hanyoyin da gwamnatin za ta rinƙa kulawa da masana’antar Kannywood a duk wata harkar cigaban jama’a idan ta taso.”
Jarumin ya yi kira ga masu harkar fim na masana’antar Kannywood da su bayar da goyon bayan su ga tsare-tsaren gwamnati yadda za ta riƙa tafiya da su a cikin harkokin ta.