• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, July 4, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Furodusa Abubakar Anka na so a farfaɗo da zumunci irin na da a tsakanin ‘yan Kannywood

by DAGA ABBA MUHAMMAD
April 24, 2023
in Labarai
0
Alhaji Abubakar Musa Anka

Alhaji Abubakar Musa Anka

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

AN yi kira ga ‘yan Kannywood, musamman na Jihar Kaduna, da su yi amfani da irin wannan lokaci na shagulgulan Sallah don sada zumunci tare da ziyartar juna kamar yadda masana’antar ta ke a baya. 

Sanannen furodusa a Kannywood, Alhaji Abubakar Musa Anka, shi ne ya bayyana hakan a lokacin tattaunawar sa da mujallar Fim don miƙa saƙon barka da Sallah.

Anka, wanda mazaunin Kaduna ne, ya ce: “Ina yi wa kowa barka da Sallah. Haƙiƙa masana’antar Kannywood a yanzu ta canza, ba kamar ta baya ba. A baya an fi mutunta juna tare da sada zumunci, musamman a lokutan shagulgulan Sallah.”

Furodusan ya ci gaba da cewa, “A baya a kan shirya wasannin Sallah. A wannan lokacin ne za a sada zumunci na haƙiƙa, domin sai ka haɗu da wanda ku ka daɗe ba ku haɗu ba. Za a ƙulla abubuwan alkhairi duk a irin wannan lokacin. A wasu lokutan kuma, har ƙulla kasuwanci da kuma ƙulla abubuwan da za su kawo wa masana’antar cigaba. Amma yanzu wasan Sallah ya zama tarihi a Kaduna.

Cewar Anka: “Yanzu wasan Sallah ya zama tarihi a Kaduna”

“Amma a wannan zamanin abubuwan sun koma duk abin da za a aiwatar sai dai a yi don a burge wani ko kuma wata. Masana’atar ta koma harkar fadanci kawai, babu ganin mutuncin juna, sai wanda ke ba ka. Wannan ba daidai ba ne.”

Anka ya yi kira ga ‘yan’uwan sa na Kannywood, musamman shugabanni, da su yi ƙoƙari wajen ganin an dawo da martabar masana’antar, an dawo da zumuncin da ake yi kamar da can baya.

Ya ƙara da cewa lallai ya kamata manyan furodusoshin Jihar Kaduna su dawo da ƙarfin su, “domin wallahi duk sun yi bacci, babu mai motsi a cikin su. Sannan kuma su yi ƙoƙari wajen dawo da irin shagulgulan Sallah da ake yi a baya.”

Anka ya ce, “Zan yi amfanin da wannan dama in miƙa saƙon barka da Sallah ga ɗaukacin ma’aikatan mujallar Fim, musamman shugaban ta, Malam Ibrahim Sheme, abokai na fudusoshin Kannywood, daraktoci, jarumai da duk wani da ke cikin masana’antar.

“Allah ya maimaita mana, ya kuma karɓi dukkan ibadun mu. Allah ya ƙara haɗa kan ‘yan Kannywood, ya kuma sa martabar ta ta dawo kamar yadda ta ke a baya.”

Loading

Previous Post

Shekara 1 da shugabancin MOPPAN a Kano: Mun samar da cigaba – Gidan Dabino

Next Post

Allah ya yi wa mahaifin furodusa Habibu Barde rasuwa

Related Posts

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

June 22, 2025
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau
Labarai

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

June 22, 2025
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

June 22, 2025
Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano
Labarai

Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano

June 20, 2025
Next Post
Marigayi Alhaji Barde Muhammad

Allah ya yi wa mahaifin furodusa Habibu Barde rasuwa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!