• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, July 7, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Hisbah ta goyi bayan soke lasisin ‘yan fim da hukumar tace finafinai ta yi

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
August 12, 2023
in Labarai
1
Sheikh Daurawa (a hagu) tare da El-Mustapha a lokacin ziyarar

Sheikh Daurawa (a hagu) tare da El-Mustapha a lokacin ziyarar

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

BABBAN Kwamandan Hukumar Hisbah ta Jihar Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, ya bayyana goyon baya ga matakin da Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta Jahar Kano ta ɗauka na ɗage lasisin dukkan masu sana’ar fim a jihar kwanan baya.

Daurawa ya yi kalamin ne a lokacin da Babban Sakataren Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano, Alhaji Abba El-Mustapha, ya kai ziyara masa ziyara a ofishin sa a ranar Laraba da ta gabata, 9 ga Agusta, 2023 don jaddada aniyar sa ta yin aiki da duk  hukumomin da su ke da alaƙar aiki da hukumar sa domin cimma nasarorin da ya sa a gaba.

Tun da aka naɗa shi shugaban hukumar kwanan nan, ya na ci gaba da ziyarar ƙulla alaƙa da hukumomin tsaro ga kula da al’amuran da su ka shafi jama’a.

Shugabannin hukumomin biyu su na musayar ra’ayi

A lokacin ziyarar da ya kai wa Darakta-Janar na Hukumar Hisbah, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, El-Mustapha ya gabatar da kan sa tare da nufin kulla alaƙar aiki a tsakanin hukumomin biyu.

A jawabin sa, ya ce: “Hukumar ta tace finafinan ta kawo wa Hukumar Hisbah ziyara ne domin neman shawarwari tare da ƙulla alaƙar aiki ta yadda hukumomin biyu za su samu fahimtar juna tare da kawo wa Jihar Kano cigaba a fannin tarbiyya tare da bunƙasar al’adu wanda kawo yanzu su ke neman zama tarihi.”

Ya kuma gode wa shugaban Hukumar Hisbah ɗin saboda lokacin da ya ba su na ziyarar tare da karrama su da aka yi.

A lokacin da ya ke mayar da jawabin sa, Sheikh Daurawa ya nuna farin ciki da zirar da aka kai masu, kuma ya gode wa El-Mustapha bisa yadda hukumar sa ta ƙwace shaidar izinin yin aiki ga duk wani abokin hulɗar ta, ya ce hakan zai taimaka tare da bai wa hukumar damar tantancewa tare da cire baragurbi a cikin masana’antar.

Daurawa ya ƙara da cewa, “Hakika akwai gurare da dama da ya kamata Hukumar Tace Finafinan ta kalla domin a yi masu gyara. Ga misali, yadda ake samar da gidajen kallo da gidajen nishaɗi, da kuma batun shigo da  ƙananan yara da kuma ɓangaren waƙoƙi da raye-raye a tsakanin maza da mata.

Ya ce saboda haka Hukumar Hisbah za ta haɗa hannu da hukumar  domin kawo sauyi tare da tsaftace ɓangarorin ta yadda jihar za ta samu cigaba.

Ya kuma yi alƙawarin ba da wakilci daga Hukumar Hisbah domin lura da yadda ake tace  finafinai don taimaka wa hukumar ta yadda za ta inganta ayyukan ta tare da cimma nasarorin da ta sa a gaba.

Jami’an hukumomin a lokacin ziyarar

Haka nan Daurawa ya  shawarci El-Mustapha da ya kafa wani sashe da zai riƙa lura da harkokin mawaƙa masu yabon Annabi Muhammadu (S.A.W) da ‘yan TikTok, da masu harkokin YouTube domin kawo gyara tare da tsaftace kalaman su ta yadda za su yi daidai da shari’ar  Musulunci.

Ya ce: “Don haka mun ƙudiri aniyar bai wa Hukumar Tace Finafinai dukkan gudunmawa tare da goyon baya ta yadda Jihar Kano da al’ummar ta za su samu cigaba.”

Loading

Previous Post

Mu na takaicin yadda wasu ‘yan fim ke nuna ɗabi’u da su ka saɓa wa addini, inji ‘yan sanda

Next Post

Jarumar Kannywood, Hauwa Kakuri, ta riga mu gidan gaskiya

Related Posts

Labarai

Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu

July 7, 2025
MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

June 22, 2025
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau
Labarai

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

June 22, 2025
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

June 22, 2025
Next Post
Marigayiya Mama Hauwa Kakuri

Jarumar Kannywood, Hauwa Kakuri, ta riga mu gidan gaskiya

Comments 1

  1. Pingback: Hisbah Ta Goyi Bayan Soke Lasisin ‘Yan Fim Da Hukumar Tace Finafinai Ta Yi » HausaMini.Com.Ng

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!