• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, August 11, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Muƙabala: Hukumar Tace Finafinai ba ta da hurumin gayyatar mawaƙa, inji lauya Abba Hikima Fagge

by MUKHTAR YAKUBU
September 18, 2025
in Labarai
0
Muƙabala: Hukumar Tace Finafinai ba ta da hurumin gayyatar mawaƙa, inji lauya Abba Hikima Fagge

Daga hagu: Shehi Mai Tajul Izzi, Abba El-Mustapha, da Abba Hikima Fagge bayan kammala zaman da suka yi a Hukumar Tace Finafinai da Ɗab'i ta Jihar Kano a yau

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

FITACCEN lauya a Kano, Abba Hikima Fagge, ya shaida wa Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta Jihar Kano cewa ba ta da hurumin gayyatar mawaƙa ko tuhumar su da aikata laifi wajen shirya muƙabala.

Hikima ya yi wannan bayanin ne a Facebook a yau bayan ya raka mawaƙin yabo Shehi Mai Tajul Izzi zuwa hukumar don amsa gayyatar da ta yi masa kan zargin sun shirya muƙabala tsakanin sa da Malam Usman Mai Dubun Isa ba bisa ƙa’ida ko neman izinin ta ba.

Mujallar Fim ta ba ku labari jiya cewa an yi muƙabalar ne a Kano a ranar Lahadi da ta gabata.

A wani saƙo da ya saki a Facebook, lauyan ya faɗi yadda suka yi da shugaban hukumar, Alhaji Abba El-Mustapha, Abba Hikima ya ce,

“Mun yi tattaunawa ta fahimta da ES Abba El-Mustapha a kan muƙabalar Mal. Shehi Mai Tajul Izzi, da Mal. Usman Mai Dubun Isa yau a ‘Censorship Board‘ wanda ya biyo bayan raɗin-raɗin hana dukkan wata muƙabala tsakanin sha’irai da kuma gayyatar mutanen biyu.

“Ina da fahimtar cewa duk da gyaran fuskar da aka yi wa dokar Hukumar Tace Finafinan ta Kano na shekarar 2025 ya ba ta hurumin kula da wani ɓangare na ayyukan sha’irai. Abin da ya faru tsakanin Mal. Shehi Mai Tajul Izzi, da Mal. Usman Mai Dubun Isa, duk da sha’irai ne, abu ne da ya shafi ‘yancin su na addini, tunani, muhawara, da bayyana wata fahimta, wadda dokokin ƙasa ya ba su damar yi. Kuma hakan idan aka yi shi cikin doka da oda zai taimaka wajen ilmantar da mutane.

“Saboda haka hukumar Shari’a Commission ko ma’aikatar addinai ita ta fi dacewa ta shiga wannan lamari ba Hukumar Tace Finafinai ba.

“Misali, duk da hukumar kula da likitoci tana da hurumi kan likitoci, za ta iya ɗabbaka wannan ƙarfi ne kawai yayin mu’amala da likitoci a aikin likitanci, ba a matsayin su na manoma ba ko ‘yan kasuwa ba.

“Saboda haka, sha’irai na da ‘yanci kamar sauran mutanen gari. Kuma kare musu ‘yanci abu ne mai muhimmanci kamar yadda taimaka musu wajen tafiyar da ayyukan su cikin bin doka da oda yake abu mai muhimmanci.”

Abba El-Mustapha (a dama) tare da Shehi Mai Tajul Izzi

A zaman nasu na yau, Malam Usman Mai Dubun Isa bai samu zuwa ba, sai dai wakilin sa ya nema masa uzirin rashin amsa gayyatar.

Loading

Previous Post

Hukumar Tace Finafinai a Kano ta haramta muhawarar mawaƙa, ta gayyaci Maidubun Isa da Tajul Izzi

Next Post

Wata jami’ar ƙasar Panama za ta ba Rarara digirin girmamawa na dakta

Related Posts

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba
Labarai

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba

August 8, 2026
Fitaccen mawaƙin siyasa Muhammadu Buhari ‘Kosan Waka’ ya kwanta dama
Labarai

Fitaccen mawaƙin siyasa Muhammadu Buhari ‘Kosan Waka’ ya kwanta dama

August 2, 2026
Yadda gwajin ƙwayoyin halitta na jini ya kawo ƙarshen auren Adam A. Zango da Maimuna Musa bayan watanni 11
Labarai

Yadda gwajin ƙwayoyin halitta na jini ya kawo ƙarshen auren Adam A. Zango da Maimuna Musa bayan watanni 11

August 1, 2026
Jami’an gwamnati sun yi zama da Kannywood domin fara aiwatar da shirin ba da inshorar lafiya kyauta ga ‘yan fim na Kano
Labarai

Jami’an gwamnati sun yi zama da Kannywood domin fara aiwatar da shirin ba da inshorar lafiya kyauta ga ‘yan fim na Kano

July 15, 2026
Kannywood tana buƙatar farfaɗo da gidajen sinima domin bunƙasa tattalin arzikin ƙirƙira – Sani Mu’azu
Labarai

Kannywood tana buƙatar farfaɗo da gidajen sinima domin bunƙasa tattalin arzikin ƙirƙira – Sani Mu’azu

July 14, 2026
A hira da mujallar Fim, mawaƙi Ado Gwanja ya aiko da saƙo ga masoyan sa daga gadon asibiti
Labarai

A hira da mujallar Fim, mawaƙi Ado Gwanja ya aiko da saƙo ga masoyan sa daga gadon asibiti

July 9, 2026
Next Post
Wata jami’ar ƙasar Panama  za ta ba Rarara digirin girmamawa na dakta

Wata jami'ar ƙasar Panama za ta ba Rarara digirin girmamawa na dakta

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!