HUKUMAR Tace Finafinai da Ɗab’i ta Jihar Kano ta haramta shirya kowace irin muhawara tsakanin mawaƙan addini ba tare da samun izinin ta ba.
Haka kuma ta gayyaci wasu mawaƙan yabon Annabi biyu, Malam Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul Izzi tare da sauran waɗanda suka jagoranci muhawarar da aka gudanar a ranar Lahadi da ta gabata da su bayyana a gaban ta cikin sa’o’i 24.
Shugaban hukumar, Alhaji Abba El-Mustapha, ya bayyana cewa wannan matakin yana daga cikin ƙoƙarin tabbatar da zaman lafiya, daidaito da kuma bin doka tsakanin mawaƙa, ko na addini ko na ɓangaren nishaɗi.
Mataki ya biyo bayan wata muhawara da aka gudanar tsakanin Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul Izzi ba tare da samun sahalewar hukumar ba, wanda hukumar ta bayyana a matsayin karya dokar ta.
Saboda haka, hukumar ta kafa kwamitin bincike ƙarƙashin jagorancin Daraktan Ayyuka na Musamman, Malam Ishak Abdullahi, inda ta umurci waɗanda suka jagoranci muhawarar da su bayyana a gaban kwamitin cikin awa 24 domin amsa tambayoyi.
Hukumar ta yi gargaɗin cewa shirya irin waɗannan muhawarori ba tare da sahalewar ta ba ya saɓa wa dokar da ta kafa ta, kuma hakan na iya jawo hukunci mai tsanani ga waɗanda suka aikata hakan.
Ta ƙara jaddada ƙudirin ta na ci gaba da sa ido a kan ayyukan mawaƙa da masu nishaɗantarwa a Kano, tare da tabbatar da bin doka da ƙa’ida.
Ta kuma buƙaci al’umma da su ci gaba da zaman lafiya, su bayar da haɗin kai da kuma kawo bayanai masu amfani domin tabbatar da zaman lafiya, fahimtar juna da cigaban al’adu a jihar.
![]()







