• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, May 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Rarara ya bada tallafin miliyan 3 ga ‘yan fim 60 saboda azumin Ramadan

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
April 15, 2021
in Labarai
0
Rarara: Fim ɗi na, ‘Gidan Dambe’, zai agaza wa ‘yan wasan Ibro
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

FITACCEN mawaƙin siyasa Dauda Adamu Kahutu (Rarara) ya raba zunzurutun kuɗi har naira miliyan uku ga wasu zaɓaɓɓu daga cikin jarumai maza da mata a masana’antar finafinan Hausa ta Kannywood su sittin.

Kowannen su zai karɓi N50,000 a matsayin tallafin azumin Ramadan da ake ciki.

Rarara, wanda kuma shi ne shugaban kamfanin Rarara Multimedia da ke Kano, ya yi hakan ne a ranar Laraba, 14 ga Afrilu, 2021.

Da ma mawaƙin ya saba bayar da irin wannan tallafin a duk shekara a daidai lokacin da ake fara azumin.

Babban sakataren kamfanin na Rarara Multimedia, Aminu Yusuf Afandaj, ya shaida wa mujallar Fim cewa, “Akwai labaran da wasu daga cikin ‘yan soshiyal midiya ke yaɗawa na cewa Rarara ya ba wa mutane hamsin tallafi na naira dubu arba’in. Ba gaskiya ba ne. Rarara ya bada umarnin zaɓo wasu daga cikin ‘yan masana’antar waɗanda su ka tsufa da kuma matsakaita a cikin ta domin ba su wannan tallafin da za su yi amfani da shi a cikin wannan watan mai albarka na Ramadan.”

Maza 20 da mata 40 aka zaɓa domin amfana da tallafin.

Mazan sun haɗa da Malam Haruna Aliyu, Bashir Nayaya (Ɗanmagori), Malam Inuwa, Bala Anas, Ɗan Azumi Baba, Hankaka, Sani Idris Kauru (Moɗa), Sani SK, Sa’idu Gwanja, Mijinyawa da AGM Bashir.

Akwai kuma Ishaq Sidi Ishaq, Ibrahim Mandawari, Bello Ibrahim (Billy O), Shehu Hassan Kano, Isa Bello Ja, Garba Gashuwa, Bawa Maikanwa, Bashir Bala (Ciroki) da Auwalu Zomuleƙa.

An umarci duk wanda ya ji sunan sa a maza da ya garzaya zuwa wajen furodusa Abubakar Bashir Maishadda domin karɓar tallafin.

A ɓangaren mata kuma akwai Hajara Usman, Asma’u Sani, Rabi Sufi Hajiya Nas, Bilkin RK, Hajiya Sadiya Arewa24, A’ishatu Mahuta, Ladidi Tubeless, Matar Mamman, Baba Duduwa, Ladidi Fagge, Halima Kara da Kiyashi, Maryam CTV da Lubabatu Madaki.

Akwai kuma Safiya Kishiya, Hindatu Bashir, Anty Fandy, Hajiyan Aisha, Rahama MK, Ummi Nuhu, Zakiyya Ibrahim, Farida Jalal, Suwaiba Makauniya, Fati Baffa Fagge, Hadiza Kabara da Hajara Abubakar (Dumɓaru).

Akwai kuma Abida Muhammad, Hafsat Shehu, Fati Al-Amin, Maryam Giɗaɗo, Jamila Gamdare, Hauwa Waraka, Fati Slow, Maimuna Mohammed (Watayarinya), Maijidda Abdulƙadir, Fati Muhammad, Zuwaira Juda, Hafsat Iliyasu da Rahama Sirace.

Alfandaj ya ce su ma matan an umarce su da duk wadda ta ji sunan ta ta karɓi nata tallafin a wurin Aisha Humaira da Ummi Ibro.

Kafin wannan tallafin, a ‘yan watannin baya mawaƙin ya bai wa wasu daga cikin maza da mata iyaye a cikin wannan masana’anta su kimanin ashirin N50,000 kowannen su. 

Haka kuma ya bai wa wasu daga cikin jaruman kyautar motoci da kuɗaɗe. Tijjani Asase da Jamila Nagudu na daga cikin waɗanda ya ba kyautar mota.

Previous Post

Gwamnati na aiki tuƙuru kan karɓo sauran ‘yan matan Chibok – Minista Sadiya

Next Post

Wa ke son ganin bayan Pantami?

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Wa ke son ganin bayan Pantami?

Wa ke son ganin bayan Pantami?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!