• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, August 10, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Aisha B. Umar ta zama shugabar matan Kannywood a Kaduna

by DAGA ABBA MUHAMMAD
April 2, 2022
in Labarai
0
Daga hagu: Aisha B. Umar, Ummulkhairi Mukhtar Usman, da Fatima Musa Abdullahi

Daga hagu: Aisha B. Umar, Ummulkhairi Mukhtar Usman, da Fatima Musa Abdullahi

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MATA masu harkar fim a Jihar Kaduna sun zaɓi tsohuwar jaruma Hajiya A’isha B. Umar a matsayin shugabar su ta riƙo a ƙarƙashin Ƙungiyar Matan Kannywood, wato ‘Kannywood Women Association of Nigeria’ (K-WAN).

Hakan ya biyo bayan kafa sabon reshen ƙungiyar a jihar.

A ranar Talata, 29 ga Maris, 2022 aka gudanar da taron kafa reshen ƙungiyar na jihar, a ƙarƙashin kwamitin amintattu (BoT), wanda ya ƙunshi su Hajiya A’ishatu Umar Mahuta da Hajiya Fatima Ibrahim Ahmad (Lamaj). 

Tun da farko dai akwai ƙungiyar ta ƙasa da Hauwa A. Bello (Edita) ke jagoranta.

Taron, wanda ya gudana a ofishin Kadawood da ke Amal Complex, Mogadishu Layout, Kaduna, an fara shi ne da misalin ƙarfe 2:50 na rana.

Tun da farko sai da Hajiya A’ishatu Umar Mahuta ta gabatar ga Malam Musa Muhammad Abdullahi, kuma ta sanar da shi tsare-tsaren su, sannan ta roƙe shi da ya sanya wa ƙungiyar albarka.

Malam Musa ya fara da yabo da kuma bayyana irin gudunmawar da marigayiya Hauwa Maina da Hajiya Fatima Ibrahim Lamaj su ka bayar a Kannywood baki ɗaya, sa’annan ya tunatar da mahalarta cewa ƙungiyar ta na tare da MOPPAN, don haka za su iya yin amfani da kundin tsarin mulkin MOPPAN.

Sai dai kuma nan take Hajiya A’isha ta sanar da shi cewa su na da nasu kundin tsarin mulkin tun tuni. Kuma ya yarda da haka.

Malam Musa ya shawarce su da cewa ya kamata su mallaki ofis na ƙungiya, sannan su rubuta wasikar gabatar ga gwamnan Jihar Kaduna da matar sa da kakakin Majalisar Dokoki ta jihar da dukkan sauran ‘yan takarar da ke neman kujera.

Daga hagu: Hadiza Maina, A’isha B. Umar, Fatima Lamaj, Fati Macijiya, A’isha Abubakar da Ummulkhairi Mukhtar Usman … bayan taron

Ya ce, “Gwamnatin Jihar Kaduna ta sha yin ƙorafi a kan yadda ƙungiyoyin masu nishaɗantarwa ba su gabatar da kan su ga gwamnati, sa’annan ya bada shawarar ƙungiyar ta rubuta wa sababbin shugabannin jam’iyyar APC wasiƙar taya su murnar samun muƙami da su ka yi.

Haka kuma ya bada shawarar su haɗa kan su, su jawo kowa a jika.

Ita ma Hajiya Fatima Lamaj ta tofa albarkacin bakin ta, inda ta yi wa Malam Musa Muhammad Abdullahi godiya da irin gudunmwar da ya ba su, sannan ta roƙe shi da ya ja kunnen membobin, kuma su ɗauki ƙungiyar da muhimmaci.

Lamaj ta yi ƙorafi game da yadda wasu matan Kannywood ke amfani da soshiyal midiya ba a bisa ƙa’ida ba, wanda ka iya taɓa mutuncin su da na industiri ɗin baki ɗaya, kuma ya taɓa raruwar su ta gaba.

A nasa ɓangaren, tsohon shugaban ƙungiyar furodusoshi ta jihar, Malam Murtala Aniya, cewa ya yi, “Mu tsaya da maganar samun membobi a yanzu, domin in mu ka ce sai ‘yan wasa mata sun yi rajista za mu iya rasa ƙarfin mu. Mu bari sai mun kafu ta yadda ƙungiyar za ta iya jan ra’ayin mutane; wannan zai sa mutane su ‘joining’ ɗin mu.”

Hajiya A’isha Mahuta kuma ta ce, “Maganar da Naziru Ahmad ya yi a kan matan Kannywood ta sa uwar ƙungiyar ta ƙasa ta ga ya dace a kafa rassa a jihohi.”

Ta yi gargaɗin cewa dukkan wata jaruma da ba ta sayi fom ba, ba za ta sha romon ƙungiyar ba, haka dukkan wani abu da ya same ta ƙungiya ba za ta tsaya mata ba.

Daga nan kuma sai aka shiga miƙa wa waɗanda aka zaɓa a matsayin shugabannin riƙo takardar shaidar kama aiki. Malam Musa Muhammad Abdullahi ne ya miƙa wa shugaba da sakatare.

A’ishatu Mahuta ta miƙa wa sakatariyar tsare-tsare da sakatariyar kuɗi, yayin da Murtala Aniya ya miƙa wa jami’ar walwala da jin daɗi da kuma mai bincike kuɗi ta 2.

Uku daga cikin shugabannin su ne: Shugaba – A’isha B. Umar; Sakatare – Ummulkhairi Mukhtar Usman, da Sakataren Tsare-tsare – Fatima Musa Abdullahi (Macijiya).

Za su riƙe ragamar ƙungiyar na tsawon shekara ɗaya da rabi ko shekara biyu.

Wasu daga cikin matan Kannywood waɗanda su ka halarci taron su ne: Hadiza Maina, A’isha Abubakar da Karima Dikko.

An tashi daga taron da misalin ƙarfe 4:30 na yamma.

Loading

Tags: A'isha AbubakarA'ishatu Umar MahutaAisha B. UmarFatima Ibrahim Ahmad LamajFatima Musa Abdullahi MacijiyafurodusoshiHadiza MainaHauwa A. BelloJihar KadunaK-WANKadawoodKannywood Women Association of NigeriaKarima DikkoKungiyar Matan Kannywoodmatan KannywoodMOPPANMurtala AniyaMusa Muhammad AbdullahiNaziru M. AhmadUmmulkhairi Mukhtar Usman
Previous Post

Ahmad Sarari ya zama mataimakin shugaban tarayyar ƙungiyoyin mashirya finafinai ta Nijeriya

Next Post

Muhammadu Gidaje, mahaifin fitattun ‘yan fim a Kaduna, ya kwanta dama

Related Posts

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba
Labarai

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba

August 8, 2026
Fitaccen mawaƙin siyasa Muhammadu Buhari ‘Kosan Waka’ ya kwanta dama
Labarai

Fitaccen mawaƙin siyasa Muhammadu Buhari ‘Kosan Waka’ ya kwanta dama

August 2, 2026
Yadda gwajin ƙwayoyin halitta na jini ya kawo ƙarshen auren Adam A. Zango da Maimuna Musa bayan watanni 11
Labarai

Yadda gwajin ƙwayoyin halitta na jini ya kawo ƙarshen auren Adam A. Zango da Maimuna Musa bayan watanni 11

August 1, 2026
Jami’an gwamnati sun yi zama da Kannywood domin fara aiwatar da shirin ba da inshorar lafiya kyauta ga ‘yan fim na Kano
Labarai

Jami’an gwamnati sun yi zama da Kannywood domin fara aiwatar da shirin ba da inshorar lafiya kyauta ga ‘yan fim na Kano

July 15, 2026
Kannywood tana buƙatar farfaɗo da gidajen sinima domin bunƙasa tattalin arzikin ƙirƙira – Sani Mu’azu
Labarai

Kannywood tana buƙatar farfaɗo da gidajen sinima domin bunƙasa tattalin arzikin ƙirƙira – Sani Mu’azu

July 14, 2026
A hira da mujallar Fim, mawaƙi Ado Gwanja ya aiko da saƙo ga masoyan sa daga gadon asibiti
Labarai

A hira da mujallar Fim, mawaƙi Ado Gwanja ya aiko da saƙo ga masoyan sa daga gadon asibiti

July 9, 2026
Next Post
Marigayi Alhaji Muhammadu Gidaje tare da ɗan sa, jarumi Sabi'u Gidaje

Muhammadu Gidaje, mahaifin fitattun 'yan fim a Kaduna, ya kwanta dama

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!