AMIRA Souley, ‘yar shekara 24 daga ƙasar Nijar, ita ce ta lashe Gasar Hikayata ta Sashen Hausa na gidan rediyon BBC ta bana.
An bayyana sakamakon gasar ne a wajen wani gagarumin biki wanda gidan rediyon ya shirya a ɗakin taro na Yar’Adua Centre da ke Abuja a daren yau.
Ban da satifiket da garkuwa, an kuma ba gwarzuwar gasar tukwicin dalar Amurka 2,000.
Wasu marubutan biyu, Hassana Labaran Ɗanlarabawa da Maryam Muhammad Sani, su ne su ka rufa mata baya a gasar, inda Hassana ta zo ta biyu, ita kuma Maryam ta zo ta uku.
Kamar yadda mujallar Fim ta ba ku labari a safiyar yau, Amira, wadda ‘yar shekara 24 ce, ta shiga gasar ne da labarin ta mai suna ‘Gudun Gara’ wanda ta shirya kan al’adar garar biki a ƙasar Hausa.
Ita kuwa Hassana ta shiga ne da labarin ‘Haihuwar Guzuma’, yayin da Maryam ta shiga da labari mai taken ‘Al’umma Ta’.
An ba Hassana tukwicin dala 1,500, aka kuma ba Maryam dala 1,000.
Maiɗakin Gwamnan Jihar Kano, Dakta Hafsat Ganduje, ita ce ta ɗauki nauyin ba su waɗannan kuɗaɗen.

A yayin da ya ke bayyana zakarun gasar, Babban Editan BBC Hausa, Malam Aliyu Abdullahi Tanko, ya sanar da cewa a bara ma Amira ta shiga gasar har ta zo ta 12.
Amira ta samu takardar shaidar malanta ta NCE daga Makarantar Bawa Jangwazo da ke Maraɗi, yanzu kuma ta na koyar da Larabci a wata makarantar firamare a Maraɗi ɗin.
Waɗanda su ka miƙa mata kyautar a kan dandamalin taron su ne Wazirin Katsina, Sanata Ibrahim Ida, da maiɗakin Gwamnan Jihar Yobe, Hajiya Gumsu Abacha Buni, da Dakta Mohammed Sani-Gwarzo, Babban Sakatare a Ma’aikatar Harkokin Jinƙai, Agaji Da Inganta Rayuwa ta Tarayya.
Gwarzuwar gasar ta yi jawabi a madadin abokan karawar ta, inda ta yi godiya ga BBC Hausa domin yadda gidan rediyon ke ba da dama ga mata su amayar da abin da ya ke cikin cikin su. Ta yi nuni da cewa matan Hausawa da dama su na da buƙatar su faɗi abin da ke ran su, amma ba su samun dama.
A wannan taro, har ila yau, an bayyana gwarazan gasar waƙar taya BBC Hausa murnar cika shekara 65.
Sha’irin da ya lashe gasar shi ne Shu’aibu Ibrahim Muhammad, wanda aka haifa a cikin 1972 a garin Lau, Jihar Taraba.
An ba shi tukwicin $2,000.
Na biyu shi ne Musa Abubakar Tunga, wanda zaɓaɓɓen kansila ne a Jihar Kebbi. An ba shi $1,500.
Ta uku ita ce fitacciyar zabiyar Kannywood, Zainab A. Baba, wadda aka ba tukwicin $1,000.
Hajiya Gumsu Abacha Buni, da tsohon Babban Hafsan Askarawan Nijeriya, Janar Tukur Yusuf Buratai, su ne su ka miƙa masa kyautar sa.
A jawabin da ya yi a madadin sauran sha’iran, Shu’aibu Ibrahim Muhammad ya ce: “Ba za mu iya kwatanta irin gudunmawar BBC Hausa ga adabin Hausa ba.”
A taron dai an gabatar da maƙaloli guda biyu a kan nasarori da tasirin Sashen Hausa na BBC, wato daga bakin Farfesa Aliyu Muhammad Bunza da Mataimakin Jami’ar Tarayya ta Kashere, Farfesa Mohammed A. Pate. Dukkan su sun kawo tarihin BBC Hausa tare da kambama tashar rediyon, kuma sun ba tashar shawarwari kan aikin da ke gaban ta a sabon ƙarni na soshiyal midiya.
Masanin waƙoƙi, Farfesa Sa’idu Muhammad, ya yi jawabi kan alƙalancin gasar mawaƙa da ya jagoranta, yayin da Dakta A’ishatu Maimota ta gabatar da jawabi kan alƙalancin Gasar Hikayata da ta gabatar.

Alƙalan Gasar Hikayata ta bana dai su ne ita Dakta Maimota da Dakta Bashir Abu Sabe da Hajiya Hauwa Lawan Maiturare da Malam Minjibir na BBC Hausa.
A tsakiyar taron an kira sananniyar mawaƙiyar nan, Khairat Abdullahi, ta rera waƙar da ta yi wa BBC Hausa kan cika shekara 65.
Mujallar Fim ta ruwaito cewa ɗimbin jama’a maza da mata sun halarci taron, kuma an ƙarƙare da cin abincin dare wanda aka wadatar da shi ga mahalarta.
An tashi daga taron ana ta haba-haba da juna.



![]()







