• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, June 4, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

An gina kabarin Umaru Kasagi kwana biyu kafin rasuwar sa, ya na da shekara 71

by DAGA EL-ZAHARADEEN UMAR DA IRO MAMMAN
October 29, 2021
in Labarai
1
Alhaji Umaru Ɗanjuma Katsina (Kasagi) (1950-2021)

Alhaji Umaru Ɗanjuma Katsina (Kasagi) (1950-2021)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

TUN shekaranjiya aka gina kabarin da aka rufe shahararren marubuci kuma ɗan wasan kwaikwayo a ciki, Alhaji Umaru Ɗanjuma Katsina (Kasagi), wanda Allah ya ɗauki ran sa a yau, inji wanda ya haƙa kabarin.

Kasagi ya rasu ne da asubahin yau bayan gajeruwar rashin lafiya, ya na da shekara 71 a duniya.

Mai haƙar kabari a maƙabartar Sabuwar Unguwa da ke Katsina, Malam Musa Ibrahim, ya faɗa wa mujallar Fim jim kaɗan bayan jana’izar Kasagi cewa an gina kabarin kwana biyu da su ka gabata don rufe wata mata da ta rasu, to amma sai ba a kawo matar wannan kushewar ba.

Kabarin Umaru Kasagi a maƙabartar Sabuwar Unguwa, Katsina

Ya ce: “Wannan kabari kwanan shi biyu. An yi shi ne da niyyar wata mata. An ce ta na da kauri… aka kawo tukunya guda aka rufe, ka gan ta can. Sai yanzu da sahe sai su ka ce mani ai Alhaji Allah ya yi mashi wa’adi. Shi kenan, sai na ce ai ko akwai ƙabarin. Su ka sawo tukwane, aka zo aka cire wa’incan aka sa nasu. To wa’incan su ne za a maida ga wancan ɗan gudun hijira.”

Ya yi addu’ar Allah ya yi wa Kasagi rahama.

Wakilin mujallar Fim ya ziyarci gidan mamacin a Sabuwar Unguwa cikin birnin Katsina, sai dai bai samu damar zantawa da wani daga cikin iyalin sa ba saboda halin kiɗimewar da su ke ciki.

Wakilin namu ya tarar da taron mutane masu zaman makoki da karɓar gaisuwa, ciki har da tsohon abokin diramar Kasagi ɗin, wato Alhaji Najume Muhammed (Idon Mujiya a wasan ‘Samanja Mazan Fama’) wanda ya bayyana alhini kan wannan babban rashi da aka yi.

Alhaji Najume, wanda cikakken sunan sa shi ne Lawal Muhammed Sani, ya bayyana cewa Kasagi ɗan’uwan sa ne na jini, kuma ɗan’uwa ne na harkar dirama inda su ka shahara.

Kasagi a cikin mujallar Fim ta Mayu 2014

Ya ce marigayin mutumin mutane ne, mai barkwanci, kuma bai rufe magana idan ya na so ya faɗe ta. Ya ce waɗannan halaye su na daga cikin dalilan da su ka sa ya ke ƙaunar shi.

Alhaji Najume ya ce haɗuwar su ta ƙarshe da Kasagi zai kai wata huɗu yanzu.

Game da dalilin rasuwar sa, ya ce da farko dai Kasagi ya yi fama da ciwo na ƙafa tsawon lokaci, ga girman shekaru, to kuma sai ya gamu da rashin lafiya inda har aka ɗan kwantar da shi a asibiti sannan da ya samu sauƙi sai aka sallamo shi. “Ashe sauƙin tafiya be,” inji shi.

 Shi dai Kasagi, ya taɓa yin cikakkiyar hira da mujallar Fim wadda aka buga a watan Mayu na shekarar 2014 inda ya bayyana tarihin rayuwar sa da ayyukan da ya yi da yadda ya shiga harkar dirama da kuma yadda ya rubuta littattafan sa na wasan kwaikwayo, wato ‘Kulɓa Na Ɓarna’ da ‘Ai Ga Irin Ta Nan’.

Hirar Umaru Kasagi a sashen Bahaushiya a cikin mujallar Fim ta Mayu 2014

Ya bayyana cewa an haife shi ne a Katsina a wajen 1950. Ya yi firamare ta ‘Central Elementary’ daga 1960-1965. 

A 1965 ya shiga ‘Provincial Secondary School’, Katsina, ya gama a 1972 bayan wani tsaiko da ya samu sakamakon rashin lafiya.

Ya fara aiki a Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta Kaduna a 1973. A lokacin ne su ka riƙa yin wasan kwaikwayo da su Ƙasimu Yero.

Da aka ƙirƙiro Hukumar Raya Al’adun Gargajiya sai aka maida shi can.

Littattafai biyu da Kasagi ya rubuta

A 1975 ya je Ingila karatun aikin silima da talabijin. Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya ta bi shi can ta ɗauke shi aiki a cibiyar ta ta raya al’adun mutanen Arewa. An ɗauke su tare da Ƙasimu Yero. 

A nan ya ci gaba da aiki har zuwa lokacin da aka ƙirƙiro Jihar Katsina a 1988, wanda ya sa ya koma Hukumar Raya Al’adun Gargajiya ta jihar a matsayin Mataimakin Darakta. 

A 1992 ya sake komawa Jami’ar Ahmadu Bello, ya ci gaba da aiki har zuwa 1992 lokacin da ya yi ritaya daga aikin gwamnati. Daga nan jami’ar ta ɗauke shi aikin kwangila, ya na koyar da yadda ake shirya dirama.

Ana zaman makoki a gidan Umaru Kasagi a Sabuwar Unguwa, Katsina, a yau

Marigayi Alhaji Umaru Ɗanjuma Katsina ya rubuta wasannin kwaikwayo ba iyaka, daga ciki aka wallafa biyu a matsayin littafi, wato ‘Kulɓa Na Ɓarna’ da kuma ‘Ai Ga Irin Ta Nan’. 

Kasagi ya ce akwai ma wasu littattafan nasa da dama waɗanda ba a buga su ba.

Memba ne a Ƙungiyar Marubuta ta Nijeriya (ANA), reshen Jihar Katsina.

Kasagi mutum ne mai tsananin son kyautata al’adun gargajiya, kuma bai gamsu da yadda ake shirya finafinan Hausa na wannan zamani ba.

Ganin sa na ƙarshe da jama’a su ka yi shi ne a wajen taron baje kolin littattafan Hausa wanda Farfesa Ibrahim Malumfashi ya shirya a Gidan Arewa, a Kaduna, mako biyu da su ka gabata.

Daga hagu: Malam Najume Muhammed (Idon Mujiya) da mai haƙa kabari Malam Musa Ibrahim

Labarin rasuwar sa ya bazu kamar wutar bazara a kafafen yaɗa labarai, inda ake ta yi masa addu’a.

Allah ya jiƙan shi, ya sa mutuwa hutu ce a gare shi, amin.

Loading

Tags: Ai Ga Irin Ta Nanal'adun gargajiyaHausa dramahausa filmsIdon MujiyaKannywoodKasagiKasimu YeroKatsinaKulba Na BarnamutuwaNajume Muhammed Idon MujiyaSabuwar Unguwa KatsinaUmaru Danjuma Katsinawasan kwaikwayo
Previous Post

Nana Firdausi, matar mawaƙi El-Bash, ta kwanta dama

Next Post

INEC ta yi wa masu zaɓe 30,449 rajista a Filato

Related Posts

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim
Labarai

MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim

June 2, 2025
Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22
Labarai

Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22

May 20, 2025
Hukuma ta rufe gidajen gala a Kano har sai bayan Ramadan
Labarai

Gwamnatin Kano ta dakatar da haska finafinan Kannywood 22 a intanet da talbijin 

May 19, 2025
Labarai

Gwamnan Kano ya ɗauki nauyin ‘yan Kannywood 5 zuwa Hajjin bana

April 17, 2025
Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu
Labarai

Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu

March 28, 2025
Next Post
INEC ta yi wa masu zaɓe 30,449 rajista a Filato

INEC ta yi wa masu zaɓe 30,449 rajista a Filato

Comments 1

  1. Musa Ibrahim says:
    4 years ago

    Allah ya rahamshe shi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!