JARUMIN Kannywood, Rabi’u Muhammad Rikadawa (Baba Ɗan Audu), ya bayyana farin cikin sa game da karramawar da ya samu daga ‘Our Nigerian News Magazine’, wanda shi kaɗai ne ya samu wannan karrama a masana’antar finafinan Hausa.
Mujallar Fim ya zanta da shi a kan wannan karramawa da ya samu na gwarzon jarumi (Best Actor), inda ya fara da cewa, “Wato a dukkanin karramawa da na ga ana yi a tsawon rayuwa ta a wannan masana’anta, zan iya cewa ni ban taɓa ganin karramawa irin wannan ba. Saboda karramawa ne wanda su su ke yi, ni ban san su ba, ko labarin su ban taɓa ji ba a duniya, su su ka bincika, su ka ji wanene ni, da me da me da me na yi? Da su ka fara ba ni labarin wasu abubuwa dangane da ni kai na, a gaskiya mamaki na yi. So, kusan dukkanin waɗanda su ka karrama a irin haka su ke zuwa.”
Dangane da yadda ya ji game da karramawar, Rikadawa ya ce, “Na yi farin ciki matuƙa, saboda in ka lura yadda su mashirya taron su ke, ‘Our Nigerian Magazine’ ne. In ka kula a irin tsarin su, kamar yadda sunan ya ke, kusan daga kowane ɓangare na rayuwa, Nijeriyan kaɗai su ke kallo. Za ka ga da su Buratai, sarakuna da sauran manyan mutane, za ka ga kowanne daga kowane sassa na Nijeriya aka ɗauko kamar yadda sunan abin ya ke. Duk irin abin da ka ke yi ko yaya ya ke, su irin abin da su ke yi kenan, su kan duba ta ina ka ke bada gudunmawa, ka ke taimakawa ƙasa, sai a karrama mutum ta irin wannan. Wannan shi ne abin burgewa da ya ba ni sha’awa. Yadda su ka ce sun duba ni, domin binciken jama’a ne, jama’a su ka zaɓa, su ka ce abin ya yi, sannan su ka ba ni.”

Jarumin ya ce ya yi matuƙar murna da farin ciki a kan wannan karramawa. Kuma na yi wa Allah godiya.
Rikadawa ya samu karramawar a matsayin na biyu kenan a wannan shekara.
A kwanakin baya an karrama shi a ‘Arewa Heroes & Philanthropic Award of Excellence’ tare da wasu jarumai da wasu manyan ƙasar nan.
Wannan taron na ‘Our Nigerian News Magazine’ an gudanar da shi ne a ranar Asabar, 11 ga Nuwamba, 2023 a ɗakin taro na International Conference Center, Abuja.


