• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 30, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ban taɓa ganin irin wannan karramawar da aka yi min ba, inji Rikadawa

by DAGA ABBA MUHAMMAD
November 15, 2023
in Labarai
0
Rikadawa riƙe da kambin karramawar sa

Rikadawa riƙe da kambin karramawar sa

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

JARUMIN Kannywood, Rabi’u Muhammad Rikadawa (Baba Ɗan Audu), ya bayyana farin cikin sa game da karramawar da ya samu daga ‘Our Nigerian News Magazine’, wanda shi kaɗai ne ya samu wannan karrama a masana’antar finafinan Hausa.

Mujallar Fim ya zanta da shi a kan wannan karramawa da ya samu na gwarzon jarumi (Best Actor), inda ya fara da cewa, “Wato a dukkanin karramawa da na ga ana yi a tsawon rayuwa ta a wannan masana’anta, zan iya cewa ni ban taɓa ganin karramawa irin wannan ba. Saboda karramawa ne wanda su su ke yi, ni ban san su ba, ko labarin su ban taɓa ji ba a duniya, su su ka bincika, su ka ji wanene ni, da me da me da me na yi? Da su ka fara ba ni labarin wasu abubuwa dangane da ni kai na, a gaskiya mamaki na yi. So, kusan dukkanin waɗanda su ka karrama a irin haka su ke zuwa.”

Dangane da yadda ya ji game da karramawar, Rikadawa ya ce, “Na yi farin ciki matuƙa, saboda in ka lura yadda su mashirya taron su ke, ‘Our Nigerian Magazine’ ne. In ka kula a irin tsarin su, kamar yadda sunan ya ke, kusan daga kowane ɓangare na rayuwa, Nijeriyan kaɗai su ke kallo. Za ka ga da su Buratai, sarakuna da sauran manyan mutane, za ka ga kowanne daga kowane sassa na Nijeriya aka ɗauko kamar yadda sunan abin ya ke. Duk irin abin da ka ke yi ko yaya ya ke, su irin abin da su ke yi kenan, su kan duba ta ina ka ke bada gudunmawa, ka ke taimakawa ƙasa, sai a karrama mutum ta irin wannan. Wannan shi ne abin burgewa da ya ba ni sha’awa. Yadda su ka ce sun duba ni, domin binciken jama’a ne, jama’a su ka zaɓa, su ka ce abin ya yi, sannan su ka ba ni.”

Janar Yusuf Tukur Buratai na miƙa wa Rikadawa kambin karramawar sa

Jarumin ya ce ya yi matuƙar murna da farin ciki a kan wannan karramawa. Kuma na yi wa Allah godiya.

Rikadawa ya samu karramawar a matsayin na biyu kenan a wannan shekara. 

A kwanakin baya an karrama shi a ‘Arewa Heroes & Philanthropic Award of Excellence’ tare da wasu jarumai da wasu manyan ƙasar nan. 

Wannan taron na ‘Our Nigerian News Magazine’ an gudanar da shi ne a ranar Asabar, 11 ga Nuwamba, 2023 a ɗakin taro na International Conference Center, Abuja.

Wani sashe na mahalarta taron
Rikadawa na jawabin godiya
Kambin karramawar Rabi’u Rikadawa

Loading

Previous Post

Mutuwar Samanja babbar asara ce ga ƙasa, inji Tinubu

Next Post

Ƙasashen Larabawa da na Musulmai sun haɗa kai wajen yin tir da hare-haren Isra’ila a Zirin Gaza

Related Posts

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

June 22, 2025
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau
Labarai

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

June 22, 2025
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

June 22, 2025
Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano
Labarai

Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano

June 20, 2025
Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza
Labarai

Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza

June 20, 2025
Next Post
Shugaba Tinubu a wajen taron na OIC

Ƙasashen Larabawa da na Musulmai sun haɗa kai wajen yin tir da hare-haren Isra'ila a Zirin Gaza

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!