MANAJAN Darakta na Hukumar Shirya Finafinai ta Nijeriya (NFC), ya gana da , Ƙaramar Ministar Gundumar Babban Birnin Tarayya, Abuja, Hajiya Mariya Mahmud Bunkure, a ofishin ta da ke Abuja, inda su ka tattauna haɗin gwiwa yayin gabatowar bikin baje-kolin finafinai na Zuma a daidai lokacin da aka fara shirye-shiryen gudanar da na wannan shekarar ta 2024.
Mujallar Fim ta ruwaito cewa akan yi bikin ne a duk shekara.
Haɗin gwiwar NFC da gwamnatin gundumar Abuja ya ta’allaƙa ne kan binciken sababbin dabaru don ɗaukaka bikin zuwa sabon matsayi.
Ali Nuhu ya duƙufa wajen inganta masana’antar finafinan Nijeriya da bunƙasa al’adun ƙirƙire-ƙirƙire da ƙwarewar sa.
A yayin gudanar da taron, shugaban na NFC ya ce, “Mu na da burin mayar da bikin finafinai na Zuma na 2024 ya zama wani muhimmin al’amari, wanda zai nuna mafi kyawun basirar mu a finafinai.
“Haɗin gwiwar NFC da ministan FCT ya na da muhimmanci mai ƙarfi wajen cimma burin mu tare da sha’awa da azama.
“Mu na shirye don gudanar bikin da ba za a manta da shi ba, wanda zai bar tarihi mai ɗorewa ga masu kallo da masu shirya finafinai.”

A nata ɓangaren, ministar ta ce ba ta da wata shakka wajen samun nasara a wannan ƙudiri na haɗin gwiwa na abokan hulɗar biyu.
Ta ba da tabbacin cewa FCT za ta taka rawar gani wajen tabbatar da an cimma manufofin bikin baje-kolin finafinan.

